Kasar Sin za ta samar da karin agajin gaggawa na yuan miliyan 100, kwatankwacin dala miliyan 14 ga kasar Venezuela, biyo bayan mummunar girgizar kasar da ta auku a kasar.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ne ya bayyana haka yayin taron manema labarai na yau Litinin, inda ya ce sabon tallafin wanda na kayayyakin agaji ne, na zuwa ne bayan tallafin kudi da tuni gwamnatin Sin ta bayar.
Ya ce nan ba da jimawa ba za a kai kayayyakin wadanda za su taimaka wa ayyukan rage radadin ibtila’in da sake gina yankunan bayan aukuwar girgizar kasar.
Baya ga haka, ya ce kasar Sin ta samar da hotunan tauraron dan Adam na wuraren da lamarin ya auku, domin tallafa wa Venezuela a ayyukan ceto. (Fa’iza Mustapha)














