Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya zargi Majalisar Dokokin Nijeriya da gaza aiwatar da dokokin da suka tsara yadda gwamnati ke karɓar bashi, yana mai cewa ’yan majalisar sun bari gwamnatoci daban-daban sun karya iyakar bashin da doka ta amince a karɓa daga Babban Bankin Nijeriya (CBN).
Sanusi, wanda tsohon gwamnan CBN ne, ya ce majalisar ta yi watsi da nauyin da kundin tsarin mulki ya ɗora mata na sa ido da takaita abin da ɓangaren zartarwa ke yi, duk da cewa akwai tanade-tanaden doka da ke iyakance bashin da gwamnati za ta iya karɓa daga babban bankin ƙasar.
Da yake magana kan muhimmancin ƙarfafa hukumomi da tabbatar da ɗaukar alhaki, Sarkin ya ce doka ta amince gwamnatin tarayya ta karɓi bashi daga CBN ne kawai har zuwa kaso biyar cikin ɗari na kuɗaɗen shiga na shekarar da ta gabata.
Ya ce: “Doka ta ce ba za a iya bayar da bashi fiye da kaso biyar cikin ɗari na kuɗaɗen shiga na shekarar da ta gabata ba. Amma an karya wannan doka ba tare da wani uzuri ba. Ina Majalisar Dokoki take? Tsawon shekaru takwas, Majalisar Dokoki ta yi shiru.”














