Labarin Lu Rongjie, jami’in JKS na kauyen Miaojia na lardin Zhejiang da ke gabashin kasar Sin da na gani a shafin jaridar intanet ta People’s Daily Online, ya tuna min da irin tsokacin da na gani a shafin sada zumunta na Facebook, bayan na wallafa wani bidiyon kauyen Caoba na gundumar Yang ta lardin Shaanxi, wadanda ke cewa, “ wannan kam ai ya girmi kauye, gwanin sha’awa” “…ki daina cewa kauye, sai ki ce kauyen birni” “yanzu nan kauye ne” da sauran makamantansu.
Irin wadannan tsokacin sun nuna irin koma bayan da har yanzu muke fama da su a yankuna da kasashenmu. A cikin ziyarce-ziyarcen da na yi a kasar Sin daga kauyuka zuwa garuruwa da manyan birane masu matukar ci gaba, yankunan kauyuka sun fi jan hankalina saboda irin ci gaban da nake ganin sun bambanta karara da abun da na saba gani.
A kauyukan kasar Sin ne za ka ga tituna da wutar lantarki tsawon sa’o’i 24 ba tare da katsewa ba, a kauyukan kasar Sin ne za ka ga sadarwar intanet da ruwan famfo sabanin abun da na saba gani a gida. A kauyukan kasar Sin ne za ka ga na’urar sanyaya wuri watau AC wadda a kasata, ko a birane, sai gidan wane da wane. A kuma kauyukan kasar Sin ne za ka ga yadda jami’ai da al’umma suka jajirce wajen yaki da talauci.Ko me ye dalilin irin wannan ci gaba da ake gani a kasar Sin? Dalilin ba ya rasa nasaba da salon shugabanci, karkashin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin wadda aka kafa ta yau shekaru 105 da suka gabata, kuma misalin shi ne jami’in jami’iyyar na kauyen Miaojia na lardin Zhejiang. Rohotanni sun bayyana cewa, mutanen kauyen ba sa kiran Lu Rongjie da sunansa, sai dai jami’in jam’iyya mai “takalman gudu,” saboda yadda yake a tafe a ko da yaushe muddun ba ya zaune a ofishinsa. Ya kan zagaye kauyen domin tattaunawa da mu’amala da jama’a saboda ya ji irin matsaloli da korafinsu ta yadda za a shawo kansu tun kafin su yi girma.
Daga inda na fito, abu ne mai wuya a samu dan siyasar da ke zagaya al’ummarsa don sanin matsalolinsu, wakiltar jama’a ya zama tamkar wani aiki na karawa kai da makusanta karfi, haka kuma ya zama tamkar wani tikitin yawace-yawacen yawon shakatawa. Na kan yi tunanin duk yawan al’ummar kasar Sin da fadin kasar, gwamnati ba ta manta da su ba. Yayin wata ziyarata a lardin Gansu shekaru 5 da suka wuce, na ziyarci wani kauye mai matukar nisa, inda a kan hanyata na yi tunanin ba za a samu abun kirki a kauyen ba. Sai dai sabanin tunanina, na tarar da kauyen na da komai na jin dadin rayuwa kamar dai sauran wuraren da na ziyarta.
Irin ayyukan da jami’an gwamnatin Sin ke yi karkashin jagorancin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya kara bayyana salon demokradiyya da shugabanci irin na kasar Sin, watau demokradiyya da ake yi domin al’umma mai hidimtawa al’umma, irin wadda ya kamata a ce kasashe masu tasowa suna koyi da ita. (Fa’iza Mustapha)














