ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Labarin Lu Rongjie: Misalin Demokradiyya Da Shugabanci Mai Hidimtawa Al’umma

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
Lu

Labarin Lu Rongjie, jami’in JKS na kauyen Miaojia na lardin Zhejiang da ke gabashin kasar Sin da na gani a shafin jaridar intanet ta People’s Daily Online, ya tuna min da irin tsokacin da na gani a shafin sada zumunta na Facebook, bayan na wallafa wani bidiyon kauyen Caoba na gundumar Yang ta lardin Shaanxi, wadanda ke cewa, “ wannan kam ai ya girmi kauye, gwanin sha’awa” “…ki daina cewa kauye, sai ki ce kauyen birni” “yanzu nan kauye ne” da sauran makamantansu.

Irin wadannan tsokacin sun nuna irin koma bayan da har yanzu muke fama da su a yankuna da kasashenmu. A cikin ziyarce-ziyarcen da na yi a kasar Sin daga kauyuka zuwa garuruwa da manyan birane masu matukar ci gaba, yankunan kauyuka sun fi jan hankalina saboda irin ci gaban da nake ganin sun bambanta karara da abun da na saba gani.

A kauyukan kasar Sin ne za ka ga tituna da wutar lantarki tsawon sa’o’i 24 ba tare da katsewa ba, a kauyukan kasar Sin ne za ka ga sadarwar intanet da ruwan famfo sabanin abun da na saba gani a gida. A kauyukan kasar Sin ne za ka ga na’urar sanyaya wuri watau AC wadda a kasata, ko a birane, sai gidan wane da wane. A kuma kauyukan kasar Sin ne za ka ga yadda jami’ai da al’umma suka jajirce wajen yaki da talauci.Ko me ye dalilin irin wannan ci gaba da ake gani a kasar Sin? Dalilin ba ya rasa nasaba da salon shugabanci, karkashin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin wadda aka kafa ta yau shekaru 105 da suka gabata, kuma misalin shi ne jami’in jami’iyyar na kauyen Miaojia na lardin Zhejiang. Rohotanni sun bayyana cewa, mutanen kauyen ba sa kiran Lu Rongjie da sunansa, sai dai jami’in jam’iyya mai “takalman gudu,” saboda yadda yake a tafe a ko da yaushe muddun ba ya zaune a ofishinsa. Ya kan zagaye kauyen domin tattaunawa da mu’amala da jama’a saboda ya ji irin matsaloli da korafinsu ta yadda za a shawo kansu tun kafin su yi girma.

ADVERTISEMENT

Daga inda na fito, abu ne mai wuya a samu dan siyasar da ke zagaya al’ummarsa don sanin matsalolinsu, wakiltar jama’a ya zama tamkar wani aiki na karawa kai da makusanta karfi, haka kuma ya zama tamkar wani tikitin yawace-yawacen yawon shakatawa. Na kan yi tunanin duk yawan al’ummar kasar Sin da fadin kasar, gwamnati ba ta manta da su ba. Yayin wata ziyarata a lardin Gansu shekaru 5 da suka wuce, na ziyarci wani kauye mai matukar nisa, inda a kan hanyata na yi tunanin ba za a samu abun kirki a kauyen ba. Sai dai sabanin tunanina, na tarar da kauyen na da komai na jin dadin rayuwa kamar dai sauran wuraren da na ziyarta.

Irin ayyukan da jami’an gwamnatin Sin ke yi karkashin jagorancin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya kara bayyana salon demokradiyya da shugabanci irin na kasar Sin, watau demokradiyya da ake yi domin al’umma mai hidimtawa al’umma, irin wadda ya kamata a ce kasashe masu tasowa suna koyi da ita. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

Lu
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel
Lu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso
  • Sulaiman
    Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI
  • Sulaiman
    Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

MASU ALAKA

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso
Daga Birnin Sin

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

July 19, 2026
Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

July 19, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026
Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

July 19, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

July 19, 2026
Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.