ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Labarin Lu Rongjie: Misalin Demokradiyya Da Shugabanci Mai Hidimtawa Al’umma

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 hours ago
Lu

Labarin Lu Rongjie, jami’in JKS na kauyen Miaojia na lardin Zhejiang da ke gabashin kasar Sin da na gani a shafin jaridar intanet ta People’s Daily Online, ya tuna min da irin tsokacin da na gani a shafin sada zumunta na Facebook, bayan na wallafa wani bidiyon kauyen Caoba na gundumar Yang ta lardin Shaanxi, wadanda ke cewa, “ wannan kam ai ya girmi kauye, gwanin sha’awa” “…ki daina cewa kauye, sai ki ce kauyen birni” “yanzu nan kauye ne” da sauran makamantansu.

Irin wadannan tsokacin sun nuna irin koma bayan da har yanzu muke fama da su a yankuna da kasashenmu. A cikin ziyarce-ziyarcen da na yi a kasar Sin daga kauyuka zuwa garuruwa da manyan birane masu matukar ci gaba, yankunan kauyuka sun fi jan hankalina saboda irin ci gaban da nake ganin sun bambanta karara da abun da na saba gani.

A kauyukan kasar Sin ne za ka ga tituna da wutar lantarki tsawon sa’o’i 24 ba tare da katsewa ba, a kauyukan kasar Sin ne za ka ga sadarwar intanet da ruwan famfo sabanin abun da na saba gani a gida. A kauyukan kasar Sin ne za ka ga na’urar sanyaya wuri watau AC wadda a kasata, ko a birane, sai gidan wane da wane. A kuma kauyukan kasar Sin ne za ka ga yadda jami’ai da al’umma suka jajirce wajen yaki da talauci.Ko me ye dalilin irin wannan ci gaba da ake gani a kasar Sin? Dalilin ba ya rasa nasaba da salon shugabanci, karkashin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin wadda aka kafa ta yau shekaru 105 da suka gabata, kuma misalin shi ne jami’in jami’iyyar na kauyen Miaojia na lardin Zhejiang. Rohotanni sun bayyana cewa, mutanen kauyen ba sa kiran Lu Rongjie da sunansa, sai dai jami’in jam’iyya mai “takalman gudu,” saboda yadda yake a tafe a ko da yaushe muddun ba ya zaune a ofishinsa. Ya kan zagaye kauyen domin tattaunawa da mu’amala da jama’a saboda ya ji irin matsaloli da korafinsu ta yadda za a shawo kansu tun kafin su yi girma.

ADVERTISEMENT

Daga inda na fito, abu ne mai wuya a samu dan siyasar da ke zagaya al’ummarsa don sanin matsalolinsu, wakiltar jama’a ya zama tamkar wani aiki na karawa kai da makusanta karfi, haka kuma ya zama tamkar wani tikitin yawace-yawacen yawon shakatawa. Na kan yi tunanin duk yawan al’ummar kasar Sin da fadin kasar, gwamnati ba ta manta da su ba. Yayin wata ziyarata a lardin Gansu shekaru 5 da suka wuce, na ziyarci wani kauye mai matukar nisa, inda a kan hanyata na yi tunanin ba za a samu abun kirki a kauyen ba. Sai dai sabanin tunanina, na tarar da kauyen na da komai na jin dadin rayuwa kamar dai sauran wuraren da na ziyarta.

Irin ayyukan da jami’an gwamnatin Sin ke yi karkashin jagorancin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya kara bayyana salon demokradiyya da shugabanci irin na kasar Sin, watau demokradiyya da ake yi domin al’umma mai hidimtawa al’umma, irin wadda ya kamata a ce kasashe masu tasowa suna koyi da ita. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ya Amsa Tambayoyi Game Da Matakan Kayyade Sayarwa Japan Kayayyaki

Xi Jinping Ya Gana Da Lukashenko

Lu
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kakakin Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ya Amsa Tambayoyi Game Da Matakan Kayyade Sayarwa Japan Kayayyaki
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Gana Da Lukashenko
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Da Philippines Na Keta Hakkoki Da Muradunta Na Teku
Lu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ya Amsa Tambayoyi Game Da Matakan Kayyade Sayarwa Japan Kayayyaki
  • Sulaiman
    Marwa Ya Kaddamar da Amfani da Bindigogin AK-47 Ga NDLEA
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Gana Da Lukashenko
  • Sulaiman
    NDLEA Ta Lalata Kilo12,234 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano

MASU ALAKA

Kakakin Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ya Amsa Tambayoyi Game Da Matakan Kayyade Sayarwa Japan Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ya Amsa Tambayoyi Game Da Matakan Kayyade Sayarwa Japan Kayayyaki

June 29, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Lukashenko
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Lukashenko

June 29, 2026
Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

June 29, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ya Amsa Tambayoyi Game Da Matakan Kayyade Sayarwa Japan Kayayyaki

Kakakin Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ya Amsa Tambayoyi Game Da Matakan Kayyade Sayarwa Japan Kayayyaki

June 29, 2026
Marwa Ya Kaddamar da Amfani da Bindigogin AK-47 Ga NDLEA

Marwa Ya Kaddamar da Amfani da Bindigogin AK-47 Ga NDLEA

June 29, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Lukashenko

Xi Jinping Ya Gana Da Lukashenko

June 29, 2026
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Lalata Kilo12,234 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 29, 2026
CBN

Majalisa Ta Yi Tsit Yayin Da Gwamnati Ke Keta Haddin Amso Bashi – Sarkin Sanusi II

June 29, 2026
Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

June 29, 2026
Labarin Lu Rongjie: Misalin Demokradiyya Da Shugabanci Mai Hidimtawa Al’umma

Labarin Lu Rongjie: Misalin Demokradiyya Da Shugabanci Mai Hidimtawa Al’umma

June 29, 2026
Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatun Biza Miliyan 1.34 Daga Hannun ’Yan Nijeriya

Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatun Biza Miliyan 1.34 Daga Hannun ’Yan Nijeriya

June 29, 2026
Yadda Yara Suka Kamo Harsasan Harbo Jirgin Sama A Yayin Kamun Kifi A Borno

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sace Ɗaliban NECO A Borno

June 29, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Da Philippines Na Keta Hakkoki Da Muradunta Na Teku

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Da Philippines Na Keta Hakkoki Da Muradunta Na Teku

June 29, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.