Kasar Sin ta nuna matukar adawa da kuma rashin gamsuwarta kan matakin da gwamnatin Burtaniya ta dauka na mayar da kamfanin mulmula karafa na British Steel ya zamo mallakar kasarta, wanda wani reshe ne na Kamfanin Jingye Group na kasar Sin, kamar yadda wani mai magana da yawun ma’aikatar kasuwanci ta Sin ya bayyana a jiya Jumma’a.Da yake bayar da amsa ga wata tambayar da manema labarai suka yi masa, jami’in ma’aikatar kasuwancin ya bayyana cewa, kamfanin mulmula karafa na British Steel ya shafe shekaru yana aiki ba tare da cin riba ba sai dai faduwa kafin Jingye ya sayi kamfanin, wanda ya zuba masa jari mai yawa har ya samu damar ci gaba da gudanar da ayyukansa da kuma rike ma’aikatansa.
Sai dai kuma, duk da haka, bangaren Burtaniya, bayan yin watsi da muhimman gudummawar da Jingye ya bayar ga tattalin arzikin kasar da al’ummarta, ya kwace kamfanin da karfin tsiya da sunan wai tsaron kasa, wanda hakan ya yi matukar danne hakkokin Jingye da muradunsa na halaliya kuma ya sanyaya gwiwar kamfanonin Sin wajen zuba jari a Burtaniya, Dangane da wannan batu kuma, a yau Asabar ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana cewa, kasar Sin na goyon bayan kamfanoni su yi amfani da hanyoyin da doka ta tanada wajen neman hakkokinsu, kuma tana sa-ido sosai kan yadda lamarin ke tafiya. Kuma za a dauki matakan kare hakkokinsu idan bukatar hakan ta taso. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














