Tsohon ɗan wasan Barcelona da Spain, Xavi Hernandez, ya ce yana da sha’awar karɓar aikin horar da wata tawagar ƙasa idan aka ba shi dama.
Xavi ya bayyana cewa zai yi maraba da duk wani tayi daga hukumar ƙwallon ƙafa ta kowace ƙasa.
Ya ce burinsa shi ne ya jagoranci tawaga a manyan gasa kamar Kofin Duniya, Gasar Cin Kofin Nahiyar Turai (Euro), Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) ko kuma Kofin Nahiyar Asiya (AFC Asian Cup).
Kocin mai shekaru 46 bai horar da wata ƙungiya ba tun bayan da ya bar Barcelona a watan Mayun 2024.
Da yake magana da gidan rediyon RNE na Spain, kamar yadda beIN Sports ta ruwaito, Xavi ya ce horar da tawagar ƙasa na ɗaya daga cikin abubuwan da yake son yi a gaba.
Ya kuma ce irin wannan aiki zai ba shi damar daidaita aikinsa da kuma bai wa iyalinsa lokaci.
A matsayinsa na koci, Xavi ya jagoranci Barcelona ta lashe La Liga da kuma Supercopa de España a kakar wasan 2022/2023.
Kafin wannan, ya horar da ƙungiyar Al Sadd ta ƙasar Qatar, inda ya lashe kofuna bakwai.
A lokacin da yake jagorancin Barcelona, ya jagoranci ƙungiyar a wasanni 143.
A matsayinsa na ɗan wasa kuwa, Xavi ya buga wa Barcelona wasanni 767, inda Lionel Messi ne kaɗai ya fi shi yawan buga wasa a tarihin ƙungiyar.
Ya kuma buga wa ƙasar Spain wasanni 133, kuma yana cikin tawagar da ta lashe Kofin Duniya na 2010, sannan ta lashe Kofin Nahiyar Turai a shekarun 2008 da 2012.
Xavi ya yi ritaya daga buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙasar Spain bayan gasar Kofin Duniya ta 2014.














