A yau Alhamis ne ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana matsayar Sin ta yin hadin gwiwa tare da kasar Bahrain, wajen ingiza manufar kawo karshen yaki, da dawo da zaman lafiya, da cimma daidaito mai dorewa a Gabas ta Tsakiya. Ya bayyana hakan ne yayin zantawa ta wayar tarho da takwaransa na Bahrain Abdullatif bin Rashid Al Zayani.
Wang Yi, ya kuma sake jaddada muhimmiyar matsayar Sin, ta nuna adawa da murdiya, tare da ingiza zaman lafiya. Ministan harkokin wajen na Sin, ya ce a baya-bayan nan kasarsa da Pakistan, sun fitar da wasu shawarwari biyar, da nufin dawo da zaman lafiya, da daidaito a yankin Gulf da Gabas ta Tsakiya, ciki har da kira da a dakatar da kaddamar da hare-hare kan fararen hula, da wuraren da ba na aikin soji ba, tare da tabbatar da tsaro a mashigin Hormuz, da kuma maido da zirga-zirga yadda ya kamata a mashigin.
A nasa tsokaci kuwa, Zayani ya bayyana yanayin tsaro da ake ciki yanzu haka a Gabas ta Tsakiya a matsayin mai cike da tarin kalubale. Ya ce an kulle mashigin Hormuz. A bangarenta kuwa Bahrain a shirye take ta taka rawar gani wajen warware batun mashigin na Hormuz, karkashin kwamitin tsaron MDD. Kazalika, Bahrain na fatan karfafa tuntubar juna, da aiwatar da tsare-tsare tare da bangaren Sin. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post