Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, ya bayyana a gaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifuffuka masu Alaƙa (ICPC) a Abuja a ranar Litinin, a matsayin wani ɓangare na binciken da ake gudanarwa kan zargin ayyukan wata hukuma PFIPC, wadda Gwamnatin Tarayya ta bayyana a matsayin hukumar bogi.
Gbajabiamila ya amsa gayyatar da hukumar ta yi masa, inda ya gudanar da wata ganawar sirri tare da Shugaban ICPC, Dakta Musa Adamu Aliyu (SAN), da kuma mambobin tawagar masu bincike a hedikwatar hukumar da ke Abuja.
Bayyanarsa a gaban hukumar na daga cikin binciken da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin gudanarwa bayan zarge-zargen cewa wata hukuma da ba a san da ita ba tana gudanar da ayyuka ta hanyar amfani da takardun gwamnati na jabu da kuma wasiƙun naɗi da ake ikirarin sun fito daga Shugaban Ƙasa.
A cikin wata sanarwa da Daraktan Wayar da Kai da Ilimantarwa na ICPC, Demola Bakare, ya fitar, ya ce Shugaban Ma’aikatar Fadar Gwamnatin ya ba da cikakken haɗin kai ga masu binciken tare da amsa tambayoyin da aka yi masa yayin zaman.
Hukumar ICPC ta ce gayyatar da aka yi wa Gbajabiamila ta yi daidai da huruminta na doka na binciken zarge-zargen cin hanci da rashawa da sauran laifuffuka masu alaƙa ba tare da nuna son kai ko wariya ba.














