Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya ce a shirye kasarsa take ta hada hannu da Korea ta Arewa wajen aiwatar da muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashe kuma shugabannin jam’iyyu masu mulkin kasashen suka cimma, domin inganta hadin gwiwa na zahiri.
Wang Yi wanda kuma mamba ne na ofishin siyasa na Kwamitin Kolin JKS, ya bayyana haka ne yau Juma’a, yayin ganawa da shugaban Korea ta Arewa Kim Jong Un, kuma sakatare janar na jam’iyyar kwadago ta kasar.
A cewar Wang Yi, yayin da ake fuskantar yanayi mai hade da sauye-sauye da rikici a duniya, ya kamata Sin da Korea ta Arewa su karfafa mu’amala da hadin gwiwa kan manyan batutuwan da suka shafi yankinsu da ma duniya baki daya. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post