Dangane da matakin da Amurka ta dauka na rashin tsawaita dokar ta-baci a matakin kasa game da yankin musamman na Hong Kong na kasar Sin, wadda wa’adinta ya kare a ranar 14 ga watan nan, ma’aikatar kasuwanci ta Sin ta bayyana a yau cewa, a yayin tattaunawar kasuwanci da aka yi a baya tsakanin Sin da Amurka a birnin Madrid, Amurka ta dauki alkawura game da batutuwan da suka shafi Hong Kong da kuma harkokin zuba jari.
Kwanan nan, Amurka ta tabbatar wa Sin cewa ba za a tsawaita wa’adin ayyana dokar ta-baci ta matakin kasa game da Hong Kong, wacce aka kafa bisa dokar bangaren zartaswar Amurka mai lamba 13936, da wa’adinta ke karewa a wannan shekara ba, kana za a kawo karshen dokar baki daya.
Wannan mataki na Amurka muhimmin ci gaba ne wajen aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma a tattaunawar cinikayya tsakanin bangarorin biyu, kuma Sin ta yaba da hakan. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














