A wani yunkuri da ake ganin an yi domin kauce wa shari’o’in da za su iya tayar da rikici a cikin jam’iyyar kafin babban zaben shekarar 2027, Jam’iyyar APC ta roki ‘yan takarar da ba su gamsu da sakamakon zaben fidda gwani da aka gudanar kwanan nan ba da kada su garzaya kotu domin kalubalantar jam’iyyar.
Ko da yake APC ba ta fito fili ta yi wannan roko ga ‘yan takarar da abin ya shafa ba, akwai alamun cewa jam’iyyar na yin hakan ne ta hanyar da ba ta fito fili ba.
Jam’iyyar APC ta jefa harkokin siyasa cikin mamaki bayan jerin sunayen ‘yan takararta da aka mika wa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) domin babban zaben 2027 suka fito fili.
Jerin sunayen ‘yan takarar kujerun Majalisar Dattawa da ta Wakilai na kunshe ne cikin wasikar da shugaban APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, da sakataren jam’iyyar na kasa, Dakta Surajudeen Ajibola Basiru, suka sanya wa hannu tare.
Jerin ya shafi mazabu bakwai na Majalisar Dattawa da kuma mazabu 19 na Majalisar Wakilai a jihohi tara da suka hada da Kogi, Abia, Binuwe, Taraba, Ondo, Neja, Kwara, Kaduna da Ebonyi. An fitar da shi ne bayan kwamitin sauraron korafe-korafe na jam’iyyar ya kammala aikinsa kan korafe-korafen da suka biyo bayan zaben fidda gwani.
Sakamakon haka, an maye gurbin fitattun ‘yan takara 26, ciki har da tsoffin gwamnoni da mambobin Majalisar Dokoki ta Kasa wadanda suka yi nasara a zaben fidda gwani, da sababbin masu daukar tutar jam’iyyar a mazabun da abin ya shafa.
A cikin wasikar da APC ta aike wa INEC, jam’iyyar ta ce an yi sauye-sauyen ne bisa shawarwarin Kwamitin Korafe-korafe kan Zaben Fidda Gwanin Jam’iyyar, tare da kara da cewa an gudanar da matakin ne daidai da Dokar Zabe ta 2026 da kuma ka’idojin INEC.
Daga cikin fitattun wadanda aka cire akwai Sanata Gabriel Suswam (Binuwe North East), wanda aka maye gurbinsa da Sanata Emmanuel Udende; tsohon Mataimakin Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam ta Nijeriya mai ritaya, Benjamin Aber (Binuwe North West), wanda aka maye gurbinsa da Sanata Titus Zam; da kuma Aro Samuel Bamidele, wanda Sanata Sunday Karimi, sanatan da ke wakiltar Kogi West a halin yanzu, ya maye gurbinsa.
Hakazalika, Prince Paul Ikonne ya maye gurbin Edinburgh Uchenna Erondu a Abia ta Kudu; Shuaibu Isa Lau ya maye gurbin Mohammed Kabir Bello a Taraba ta Arewa; Adeniyi Adegbonmire ya maye gurbin Taiwo Fasoranti a Ondo ta Tsakiya; yayin da Olajide Ipinsagba ya maye gurbin Gbenga Elegbeleye a Ondo ta Arewa.
A Majalisar Wakilai kuwa, an samu sauye-sauye da dama a Jihar Binuwe. A mazabar Makurdi/Guma, Hon. Dickson Tarkighir ya maye gurbin Ikper Chris Terfa; a Bandeikya/Konshisha, Hon. Sesoo Ikpagher ya maye gurbin Libinus Tsar Adzor; a Kwande/Ushongo, Hon. Terser Ugbor ya maye gurbin Kohol Shedrach Iornem; a Buruku, Hon. Sekab Iyortyom ya maye gurbin Gideon Inyom; yayin da a Gwer East/Gwer West, Hon. Austin Asema Achado ya maye gurbin Nongo Dabid.
A mazabar Gashaka/Kurmi/Sardaunan Taraba, Peter Abel Diah ya maye gurbin Sanusi Mohammed Galadima.
A mazabar Suleja/Tafa/Gurara ta Jihar Neja, Abubakar Lado Abdullahi ya maye gurbin Adamu Tanko, yayin da a Labun/Edati/Mokwa, Adamu Suleiman ya maye gurbin Adamu Usman.
A Ekiti/Irepodun/Oke-Ero ta Jihar Kwara, Raheem Tunji Olawuyi ya maye gurbin Olasumbo Florence Oyeyemi, yayin da a Edu/Patigi/Moro, Mohammed Mamman ya maye gurbin Bello Tauheed Abubakar.
Jihar Ondo ma ta samu gagarumin sauyi a mazabar Ilaje/Ese-Odo, inda Donald Ojogo ya maye gurbin Akingboye Leke.
Haka kuma, a Idanre, Festus Olarewaju ya maye gurbin Rasak Obe; a Owo/Ose, Oluwatimehin Akintomide ya maye gurbin Kayode Ijalana; a Okitipupa/Irele, Okunjinmi John Odimayo ya maye gurbin Olumuyiwa Daramola; a Ondo West/Ondo East, Michel Olamidotun Akintomide ya maye gurbin Abiola Makinde; yayin da a Ile-Oluji/Oke-Igbo/Odigbo, Festus Ayodele Adefiranye ya maye gurbin Oyerinmade Matthew.
Haka kuma, a Kaduna ta Arewa, Abdulazeez Kaka ya maye gurbin Samaila Abdu Suleiman; a mazabar Ukwa East/Ukwa West ta Jihar Abia, Samuel Okezie ya maye gurbin Chris Nkwonta; yayin da a mazabar Afikpo North/Edda ta Jihar Ebonyi, Ekumankama Joseph Nkama ya maye gurbin Hon. Iduma Igariwey Enwo, Mataimakin Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Wakilai.
Bayan an yi nazari kan rahotannin kwamitin sauraron korafe-korafen kuma aka tura sabon jerin sunayen ga Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), jam’iyyar APC ta kammala tsarin tsayar da ‘yan takararta.
Sakataren Yada Labarai na APC na Kasa, Felid Morka, ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da manema labarai kwanan nan, inda ya ce babban abin da jam’iyyar ta fi mayar da hankali a kai shi ne tabbatar da cewa dukkan ‘yan takararta sun cike takardun tsayawa takara na INEC domin dora su a shafin Intanet na hukumar.
Morka ya bayyana cewa jam’iyyar ta karbi korafe-korafe sama da 700 daga ‘yan takarar da ba su gamsu ba, wadanda suka yi zargin cewa an tauye musu hakkinsu a tsarin zaben fidda gwani a mazabu daban-daban.
Kakakin APC ya kara da cewa jam’iyyar ta yi cikakken nazari kan kowace korafi cikin tsanaki, lamarin da ya haifar da sauya wasu daga cikin ‘yan takarar da tun farko suka yi nasara a zaben fidda gwani.
Takardar korafin, wacce shugaban APC na shiyyar Kogi ta Yamma, Emmanuel Aledare ya sanya wa hannu tare da Mataimakin Shugaban APC na Jihar Kogi, Aliyu Salihu, da Shugaban Matasa na Jihar, Buhari Lokoja, ta bayyana maye gurbin dan takarar a matsayin abin da ya saba wa doka, wanda kuma zai iya raunana hadin kan jam’iyyar gabanin babban zaben shekarar 2027.
Sai dai domin kauce wa shigar da kara a kotu, Felid Morka ya ce jam’iyyar ta fara amfani da tsarin sasanta rikice-rikice na cikin gida domin magance korafe-korafen ‘yan takarar da ba su gamsu ba.
Ya ce, “Jam’iyyar ta fara amfani da tsarin sasanta rikice-rikice na cikin gida, kuma muna samun gagarumin ci gaba.”
Morka ya sake jaddada wannan matsayi a wannan makon yayin wata hira da tashar ARISE NEWS, inda ya amince cewa wasu ‘yan takara ba su gamsu da sakamakon zaben fidda gwani ba, amma ya ce jam’iyyar na aiki tukuru domin rage damuwarsu.
Ya ce, “Idan mutum bai yi nasara ba, a dabi’ance yana iya jin rashin dadi. Shi ya sa muka dauki lokaci muka bi dukkan matakan sauraron korafe-korafe domin tabbatar da cewa babu wata korafi da ba mu yi cikakken nazari a kanta ba.”
Morka ya kuma bayyana cewa jam’iyyar ta fara tattaunawa da ‘yan takarar da ba su gamsu ba domin tabbatar musu cewa tsarin ya kasance cikin gaskiya kuma ba a gudanar da shi bisa son rai ko fifita wasu ba.
Ya ce, “Abin da muke gaya musu shi ne ba kowa ne zai zama mai daukar tutar jam’iyya ba. Mun riga mun fara tattaunawa da irin wadannan mutane domin tabbatar musu cewa ba batun daukar fansa ko son rai ba ne. Babu abin da aka yi ba bisa ka’ida ba, kuma ba a fifita kowa wajen ba shi tikitin takara.”
Ko da yake jam’iyyar ba ta fito fili ta yi kira ga wadanda abin ya shafa da kada su kai kara kotu ba, akwai alamun cewa tana yin wannan roko a boye ta hannun shugabanninta.
Wani babban jigo a APC da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa LEADERSHIP Weekend cewa: “Tabbas, jam’iyyar na tuntubar wasu daga cikin wadanda abin ya shafa ta hannun shugabanninmu a jihohinsu. Muna son su fahimci dalilan da ya sa bai dace su zabi hanyar shari’a ba a wannan lokaci mai muhimmanci, domin muna bukatar hada kan jam’iyya kafin babban zaben shekarar 2027.”
Wani babban jigon jam’iyyar, wanda shi ma ya nemi a sakaya sunansa, ya ce APC na la’akari da yadda za ta lallashi ‘yan takarar da ba su gamsu ba ta hanyar ba su mukaman gwamnati ko kuma saka su cikin kwamitocin yakin neman zaben shekarar 2027.
Ya ce, “Jam’iyyar ba kawai tana gaya musu su manta da abin da ya faru ba ne. APC ce ke mulkin gwamnatin tarayya kuma tana da rinjaye a mafi yawan jihohi. Saboda haka, wadanda abin ya shafa za a iya ba su mukamai a hukumomin gwamnati ko kuma a sanya su cikin kwamitocin yakin neman zabe.”
Wasu manyan jiga-jigan APC biyu a Jihar Oyo, Sanata Olufemi Lanlehin da Farfesa Taoreed Adedoja, sun tabbatar wa mambobin jam’iyyar cewa, “Babu wani dan takarar da bai gamsu ba da za a bari a baya a kokarin sasanta rikicin da ake yi.”
Su biyun sun bayyana hakan ne yayin jawabansu na karbar mukaman shugaban da mataimakin shugaban Kwamitin Sasanta Rikicin APC na Jihar Oyo a Ibadan. Sun kuma yaba wa Kwamitin Zartarwa na Jam’iyyar na Jiha karkashin jagorancin Moses Adeyemo bisa kafa kwamitin, suna mai cewa matakin ya zo a kan lokaci.
Adeyemo ya bukaci mambobin kwamitin da su yi amfani da kyakkyawar alakarsu, hikimarsu da gogewarsu wajen warware korafe-korafen da suka taso daga tarukan jam’iyyar da zaben fidda gwani na baya-bayan nan, domin APC ta shiga zabukan da ke tafe cikin hadin kai da karfi.
Ya ce: “Mun san cewa sakamakon tarukan jam’iyyar da aka gudanar, wadanda suka samar da shugabannin jam’iyyar a matakai daban-daban, da kuma zaben fidda gwani na baya-bayan nan da ya samar da ‘yan takarar 2027, sun haifar da rashin jin dadi a tsakanin wasu mambobi da masu ruwa da tsaki. Amma ba ma son wannan ya rikide ya zama rikicin da ba za a iya shawo kansa ba, wanda zai lalata damarmu a zabe.
“A namu bangaren, a shirye muke mu tattauna da wadanda ba su gamsu ba domin ganin abin da za mu iya yi don rage damuwarsu.
“Mun san koke-koken suna da yawa ne saboda APC ita ce jam’iyyar da ake ganin za ta fi kowace jam’iyya karfi a kowane zabe a kasar nan. Amma ba ma son mu yi sakaci a wannan lokaci, domin burinmu shi ne mu samar wa Shugaba Bola Tinubu kuri’u miliyan daya, tare da dawo da APC Gidan Gwamnatin Agodi a shekara mai zuwa.”














