A yau Jumma’a 17 ga watan Yuli, shugaban kasar Sin, Xi Jinping, ya gana da babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya (MDD), António Guterres, a birnin Shanghai. Guterres ya ziyarci kasar Sin ne domin halartar taron duniya kan fasahar AI na shekarar 2026 da kuma taron manyan jami’ai game da tafiyar da sha’anin AI a duniya.
Xi Jinping ya bayyana cewa, kamar yadda ta saba, kasar Sin za ta kara karfafa hadin gwiwa da Majalisar Dinkin Duniya domin karfafa manufar zaman lafiya da ci gaban duniya, tare da inganta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga bil’adama.
A nasa bangare, Guterres ya bayyana cewa, kasar Sin ta ci gaba da yin tsayin daka wajen nuna cikakken goyon baya ga tsarin hadin kan mabambantan bangarori, da ayyukan Majalisar Dinkin Duniya, da kuma hadin gwiwar kasa da kasa, inda ta zama abar koyi ga sauran kasashen duniya. Majalisar Dinkin Duniya za ta ci gaba da karfafa hadin gwiwa da kasar Sin domin kare muradun al’ummar duniya na bai-daya.
Kana ya gana da firaministan Thailand, Anutin Charnvirakul a birnin Shanghai. Anutin ya ziyarci kasar Sin ne domin halartar taron duniya kan fasahar kirkirarriyar basira ta AI na shekarar 2026 da kuma babban taron manyan jami’ai game da tafiyar da sha’anin fasahar AI a duniya, kana da gudanar da ziyarar aiki a kasar.
Xi Jinping ya bayyana cewa, ya kamata kasar Sin da Thailand su hanzarta gina layin dogo da zai sada kasashen biyu da kuma hade layin dogo na tsakanin Sin, da Laos, da kuma Thailand, tare da fadada hadin gwiwa a sabbin fannoni kamar fasahar AI, da harkar sararin samaniya, da makamashi mai tsafta.
A nasa bangaren, Anutin ya bayyana cewa, kasar Thailand a shirye take ta karfafa hadin gwiwa da kasar Sin domin karfafa zaman lafiya, da kwanciyar hankali, da ci gaba, da samun wadata a yanki da ma duniya baki daya.
Kazalika, duk da a yau din, Xi Jinping ya gana da firaministan Cambodia, Hun Manet, wanda shi ma ya zo kasar Sin ne domin halartar taron duniya kan fasahar kirkirarriyar basira ta AI na shekarar 2026. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














