Bisa gayyatar kwamitin tsakiyar jam’iyyar ‘yan kwadago ta Koriya ta Arewa da gwamnatin Koriya ta Arewa, memban kwamitin dindindin na ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar jam’iyyar kwaminis ta Sin JKS, kuma shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siaysa ta kasar Wang Huning, ya jagoranci tawagar wakilai domin ziyarar aiki a Koriya ta Arewa daga ranar 15 zuwa 17 ga watan Yuli.
A birnin Pyongyang, ya gana da babban sakataren jam’iyyar ‘yan kwadago ta Koriya ta Arewa, kuma shugaban kasar Kim Jong-un.Wang Huning ya isar da sahihiyar gaisuwar shugaban kasar Sin Xi Jinping ga Kim Jong-un yayin ganawar tasu.
Wang Huning ya bayyana cewa, bana ita ce ta cika shekaru 65 da sanya hannu kan “Yarjejeniyar abota da hadin gwiwa tsakanin Sin da Koriya ta Arewa”. Ziyarar da shugaba Xi ya kai Koriya ta Arewa kwanan nan, ta samu cikakkiyar nasara. Shugabannin biyu sun gudanar da tattaunawa mai zurfi, kuma sun cimma jerin muhimman yarjejeniyoyi, wadanda suka kafa kyakkyawar makoma ga ci gaban dangantakar Sin da Koriya ta Arewa a sabon zamani, da kuma kara wa ayyukan gurguzu na kasashen biyu kuzari.
A nasa bangare, Kim Jong-un ya mika gaisuwarsa ga shugaba Xi, ya kuma taya jam’iyyar kwaminis ta Sin murnar cika shekaru 105 da kafuwa.
Kim Jong-un ya kara da cewa, bangaren Koriya ta Arewa zai ci gaba da dora babban muhimmanci kan raya dangantakar Koriya ta Arewa da Sin, kuma zai kara tunbubar manyan shugabanni da bangaren Sin, da zurfafa musayar ra’ayi kan dabarun gudanar da harkokin jam’iyya, da karfafa amincewar siyasa tsakaninsu, da kuma fadada hadin gwiwa a fannoni kamar tattalin arziki, da fasaha, da kiwon lafiya, da al’adu da sauransu, domin amfanar da al’ummomin kasashen biyu.(Amina Xu)













