ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

by Sani Anwar
59 minutes ago
APC

Tsohon dan majalisar wakilai, Farfesa Haruna Yerima, ya ce; yadda Shugaba Bola Tinubu ya ci gaba da rike Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa a zaben 2027, zai haskaka damar da jam’iyyar APC ke da ita a dukkanin matakai.

Ya kara da cewa, Shettima ya kasance mai biyayya ga Shugaba Bola Tinubu kwarai da gaske. “A rubuce yake cewa, Sanata Kashim Shettima, ya kasance mataimakin Shugaba Tinubu mai aminci da kwarewa, wanda ko kadan ba shi da hayaniya.

“Ko masu sukarsa a siyasa, ba za su iya musanta gaskiyar cewa; shi kwararren mai karfin tunani ba ne.”

ADVERTISEMENT

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya bayyana Sanata Shettima a ranar Juma’a lokacin da ya karbi sunayen Shugaba Tinubu da Shettima, domin mika su ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin siyasa, Alhaji Ibrahim Masari, ya mika sunayen biyu a wani takaitaccen biki da ya samu halartar mambobin kungiyar gwamnonin (PGF), majalisar dokoki ta kasa, majalisar zartarwa ta tarayya (FEC), mambobin kwamitin aiki na kasa na APC (NWC), shugabannin jam’iyyar na jihohi da wasu ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar a Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Farfesa Yerima ya ce, Shugaba Tinubu ya zabi Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, bayan la’akari sosai da wasu dalilai daban-daban.

“Shugaba Tinubu, ya zabi Sanata Shettima don taimaka masa wajen aiwatar da wannan ajanda.” Wannan ya faru ne, bayan nazari mai zurfi a kan ayyukansa cikin shekaru uku da suka gabata,” in ji jigon na APC.

Tsohon dan majalisar ya ce, “Mataimakin shugaban kasa Shettima, bisa ga dukkan ka’idoji, mutum ne mai himma, mai biyayya da jajircewa, kuma kwararren masanin ilimi, wanda ke da ingantattun takardun dimokuradiyya.”

“Sanata Shettima ya fahimci yanayin sosai, ta hanyar ci gaba a matsayin malamin jami’a (shekaru 2), ma’aikacin banki (shekaru 6), kwamishina a ma’aikatu da dama a Jihar Borno (shekaru 4), zababben gwamna (shekaru 8), sanata (shekaru 4), kafin ya kai matsayinsa na mataimakinka mai aminci da kuma himma,” in ji Farfesa Yerima.

Jami’in ya ce, Sanata Shettima ya kasance mai goyon baya da kuma goyon bayan ka’idojin Shugaba Tinubu, manufofi, gyare-gyare da sauye-sauye a kowane lokaci, a kuma ko’ina.

“Ya halarci tarukan zabe na 2023 a fadin kasar nan, kuma ya taka muhimmiyar rawa da muka gani a lokacin zaben shugabannin majalisar dokoki ta kasa, wanda ya ga fitowar ‘yan takarar da jam’iyya mai mulki ta amince da su,” in ji shi.

Ya gode wa Shugaba Tinubu, sakamakon abubuwa masu yawa da ya yi masa da kuma biyayya da amincewa.

APC
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala
Labarai

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON
Labarai

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Next Post
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.