Tsohon dan majalisar wakilai, Farfesa Haruna Yerima, ya ce; yadda Shugaba Bola Tinubu ya ci gaba da rike Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa a zaben 2027, zai haskaka damar da jam’iyyar APC ke da ita a dukkanin matakai.
Ya kara da cewa, Shettima ya kasance mai biyayya ga Shugaba Bola Tinubu kwarai da gaske. “A rubuce yake cewa, Sanata Kashim Shettima, ya kasance mataimakin Shugaba Tinubu mai aminci da kwarewa, wanda ko kadan ba shi da hayaniya.
“Ko masu sukarsa a siyasa, ba za su iya musanta gaskiyar cewa; shi kwararren mai karfin tunani ba ne.”
Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya bayyana Sanata Shettima a ranar Juma’a lokacin da ya karbi sunayen Shugaba Tinubu da Shettima, domin mika su ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).
Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin siyasa, Alhaji Ibrahim Masari, ya mika sunayen biyu a wani takaitaccen biki da ya samu halartar mambobin kungiyar gwamnonin (PGF), majalisar dokoki ta kasa, majalisar zartarwa ta tarayya (FEC), mambobin kwamitin aiki na kasa na APC (NWC), shugabannin jam’iyyar na jihohi da wasu ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar a Abuja.
Farfesa Yerima ya ce, Shugaba Tinubu ya zabi Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, bayan la’akari sosai da wasu dalilai daban-daban.
“Shugaba Tinubu, ya zabi Sanata Shettima don taimaka masa wajen aiwatar da wannan ajanda.” Wannan ya faru ne, bayan nazari mai zurfi a kan ayyukansa cikin shekaru uku da suka gabata,” in ji jigon na APC.
Tsohon dan majalisar ya ce, “Mataimakin shugaban kasa Shettima, bisa ga dukkan ka’idoji, mutum ne mai himma, mai biyayya da jajircewa, kuma kwararren masanin ilimi, wanda ke da ingantattun takardun dimokuradiyya.”
“Sanata Shettima ya fahimci yanayin sosai, ta hanyar ci gaba a matsayin malamin jami’a (shekaru 2), ma’aikacin banki (shekaru 6), kwamishina a ma’aikatu da dama a Jihar Borno (shekaru 4), zababben gwamna (shekaru 8), sanata (shekaru 4), kafin ya kai matsayinsa na mataimakinka mai aminci da kuma himma,” in ji Farfesa Yerima.
Jami’in ya ce, Sanata Shettima ya kasance mai goyon baya da kuma goyon bayan ka’idojin Shugaba Tinubu, manufofi, gyare-gyare da sauye-sauye a kowane lokaci, a kuma ko’ina.
“Ya halarci tarukan zabe na 2023 a fadin kasar nan, kuma ya taka muhimmiyar rawa da muka gani a lokacin zaben shugabannin majalisar dokoki ta kasa, wanda ya ga fitowar ‘yan takarar da jam’iyya mai mulki ta amince da su,” in ji shi.
Ya gode wa Shugaba Tinubu, sakamakon abubuwa masu yawa da ya yi masa da kuma biyayya da amincewa.














