Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun, ya ce kasarsa ta lura da furuci na baya-bayan nan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi game da yankin Taiwan.
Da yake tsokaci kan furucin Donald Trump yayin taron manema labarai na yau Litinin, Guo Jiakun ya ce Taiwan wani bangare ne na kasar Sin da ba zai iya ballewa ba, ba ta taba zama kasa ba, kuma ba za ta taba zama ba a nan gaba.
Ya ce mahukuntan Taiwan karkashin Lai Ching-te, da suke kokarin shigar da batun Taiwan cikin harkokin kasa da kasa, su ne manyan masu kokarin sauya matsayin da ake kai, kuma su ne ainihin masu haifar da rashin kwanciyar hankali a zirin Taiwan.
Da yake bayar da amsa ga tambayoyin manema labarai game da yunkurin Taiwan na shiga harkokin babban taron hukumar lafiya ta duniya (WHA), Guo Jiakun ya ce kasar Sin daya ce tak a duniya, kuma Taiwan wani bangare ne na kasar.
Ya kara da cewa, gwamnatin Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin, ita ce halastacciyar gwamnati daya tilo da ke wakiltar dukkan kasar Sin.
Ya kuma nanata cewa, wajibi ne hukumomin kasa da kasa kamar WHO, su rika tafiyar da harkokin da suka shafi Taiwan bisa kiyaye ka’idar kasar Sin daya tak. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post