Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi tsohon uban gidansa, Rabiu Musa Kwankwaso, da ya daina yi masa kalamai marasa daɗi ko kuma ya fara mayar masa da martani.
Abba ya ce kada mutane su ɗauki shirun da yake yi a matsayin tsoro.
Ya bayyana cewa yana haƙuri ne saboda girmamawa da ladabi.
Wannan shi ne karon farko da gwamnan ya fito fili yana magana kan saɓanin da ke tsakaninsa da Kwankwaso tun bayan rabuwar siyasarsu a farkon shekarar nan.
A kwanakin baya, Kwankwaso ya yi hira da gidan talabijin na Trust TV inda ya ce shi ne ya taimaka wa Abba Kabir har ya zama gwamna.
Ya kuma ce wata rana Abba zai yi nadamar rabuwa da shi.
Sai dai yayin wani taro a garin Rano na tabbatar da Sulaiman Kawu Sumaila a matsayin ɗan takarar Sanatan Kano ta Kudu a jam’iyyar APC, Abba Kabir ya ce idan aka ci gaba da matsa masa, zai fara bayyana wasu abubuwa da mutane ba za su so ji ba.
Ya ce:“Shirunmu ba tsoro ba ne. Mutum mai shekara 69 bai kamata yana kiran mai shekara 63 yaro ba.”
Gwamnan ya ƙara da cewa idan dattijo bai mutunta kansa ba, matasa ma za su samu abin faɗa.
Haka kuma ya roƙi magoya bayan Kwankwasiyya da su guji kalaman da za su iya jawo rikici ko tonon asiri.















Discussion about this post