Kwanan baya, shugaban majalisar dokokin kasar Georgia Shalva Papuashvili ya yi ziyarasa ta farko a kasar Sin, inda ya ziyarci birnin Beijing da lardin Shaanxi. A cewarsa, “Ga kasashe da dama a duniya, Sin ta zama abin koyi na sauyi da ci gaban su, ko ta fuskar siyasa, da tattalin arziki ko kuma zamantakewa.”
Mr.Papuashvili ya bayyana haka ne yayin tattaunawarsa da wakiliyar babban rukunin gidajen rediyo da talibijin na kasar Sin, wato CMG a takaice, inda ya kuma yaba wa muhimmiyar rawa ta musamman da kasar Sin ke takawa a dandamalin kasa da kasa.
A cewarsa, “A ko da yaushe, Sin tana rike da matsayin kiyaye zaman lafiya da dokokin kasa da kasa. Hakan ya shaida cewa, wata kasa, musamman ma babbar kasa, ba lallai ne ta yi amfani da karfin makamai don neman ci gabanta ba, kuma ba bukatar ta yi barazana a fannin, ko kuma ta dauki neman karfin soja a matsayin hanya daya tilo ta zama babbar kasa a duniya.
Ya ce Sin ta nuna wa duniya cewa, bin manufar zaman lafiya ba wai kawai yana samun karbuwa daga sassa daban daban ba, har ma ya nuna cewa, yayin da wata kasa ta himmantu kan ci gaban kanta, a lokaci guda, tana iya taimakawa sosai wajen ci gaban yankunan da ke kewaye da ita, har da duniya baki daya. (Bilkisu Xin)















Discussion about this post