Gwamnatin Ghana ta bayyana cewa za ta kai ƙarar gwamnatin Canada gaban Kotu saboda hana ɗan wasan ƙwallon ƙafarta, Thomas Partey, shiga ƙasar.
A wata sanarwa da ta fitar, gwamnatin Ghana ta ce wannan mataki ba adalci ba ne, kuma za ta ƙalubalanci hukuncin a kotu.
Rahotanni sun ce an hana Partey shiga Canada ne saboda wasu shari’ar da ake yi masa a Birtaniya kan zargin cin zarafin mata.
Sai dai gwamnatin Ghana ta ce har yanzu ba a kammala waɗannan shari’o’i ba, kuma ba a same shi da wani laifi ba.
An hana Partey shiga Canada ne a daidai lokacin da tawagar ƙwallon ƙafar Ghana ke shirin fara buga gasar cin kofin duniya da Panama a ranar Alhamis.
Gwamnatin Ghana ta jaddada cewa babu wata kotu da ta yanke wa Partey hukuncin laifi zuwa yanzu.
Saboda haka, ta ce za ta bi duk hanyoyin shari’a domin a soke matakin da Canada ta ɗauka.















Discussion about this post