A yau Litinin gwamnatin kasar Sin ta fitar da sanarwa game da shirinta na aiwatar da wasu matakai na inganta mayar wa baki da ke shirin fita daga kasar kudaden harajin sayayya da suka yi, ciki har da kara yawan kantunan mayar da kudaden harajin, da tsarin sanya ido kan manhajojin mayar da kananan kudaden harajin da ake mayarwa, da kyautata hidimomin mayar da kudaden harajin sayayya na nan take.
A yau na kara fahimtar cewa manufar bude kofa da kasar Sin ke aiwatarwa ba ta tsaya kadai ga jan hankalin baki ’yan kasuwa da masu zuba jari ba, kyakkyawar manufa ce da ake aiwatarwa a aikace, wadda kuma ta shafi kowa da kowa.
Hakika kasar Sin tana kara nuna wa al’ummar duniya cewa, tana maraba da su sabanin yadda wasu kasashe ke kara tsaurara matakai na nuna wariya da rufe kofa.
Baya ga aiwatar da matakan soke visa ga jama’ar wasu kasashe har na tsawon kwanaki 30, tsarin da take daukaka wa na mayar da haraji, wata hanya ce ta kara jan hankalin masu ziyara zuwa kasar.
A ganina wannan wata dama ce ga al’ummar duniya ta shigowa domin gane wa idanunsu ci gaban kasar Sin da fahimtar yanayinta da al’adunta da ma yadda take tafiyar da harkokinta da kula da al’ummarta.
Karkashin wannan manufa, masu ziyara za su ji dadin yin sayayya baya ga bude ido a kasar mai tarin abubuwan al’ajabi da ban mamaki. Haka kuma cikin sauki za su iya karbar harajin da za a mayar musu tun da yanzu an samar da hanyoyin mayar da kudin ta wayoyin salula kuma a wuri guda ba tare da jira sai an je filayen jiragen sama ko dukkan wuraren da aka yi sayayya ba.
Bugu da kari, rage yawan kudin daga RMB 500 zuwa 200, wani karin kwarin gwiwa ne na yin sayayya wanda zai kara bayar da gudunmuwa ga habaka tattalin arzikin kasar.
Irin wannan shi ake kira da moriyar juna. Watau masu sayayya sun more, ita ma kasar Sin ta amfana, kuma kayayyakinta za su kara shiga duniya da samun karbuwa.Kasar Sin ta nuna cewa ci gaba, baya nufin rufe kofa da nuna fifiko.
Ci gaba na nufin bude kofa, kara mu’amala da fahimta tsakanin jama’a, haka kuma ci gaba na nufin cin moriyar juna maimakon samun riba daga faduwar wani. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post