Tsohon shugaban masu rinjaye na majalisar dattawa, Ali Ndume, ya samu tikitin takarar sanatan Borno ta kudu na jam’iyyar APC bayan an ayyana shi a matsayin ɗan takara ta hanyar sulhu.
An tabbatar da Ndume a matsayin ɗan takara ne a wajen zaɓen fidda gwani da aka gudanar a Maiduguri, bayan babban abokin hamayyarsa, Abdullahi Askira, ya janye daga takarar a watan da ya gabata sakamakon roƙon shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki a yankin.
Abdullahi Askira, wanda shi ne mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Borno, ya bayyana cewa ya haƙura da takarar ne bayan tattaunawa da shawarwari daga manyan jam’iyyar a shiyyar tasu.
Idan Ali Ndume ya yi nasara a babban zaɓen 2027, hakan zai ba shi damar komawa majalisar tarayya karo na biyar.
Bayan bayyana shi a matsayin wanda ya lashe tikitin, Ndume ya gode wa shugabannin APC, da wakilai da magoya bayan jam’iyyar a Borno ta Kudu bisa amincewar da suka nuna masa, yana mai alƙawarin ci gaba da kare muradun al’ummar yankin a majalisar tarayya.















Discussion about this post