Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Mao Ning ta bayyana cewa hadin gwiwar tattalin arziki da ciniki tsakanin Sin da Tarayyar Turai, ya samo asali ne daga burin cimma muradun bai daya, kuma jigonsa shi ne samar da fa’ida a fannin gogayyar kasuwa.
Don haka ake fatan Tarayyar Turai za ta dauki dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da Sin bisa sahihiyar matsaya, kuma ta yi aiki tare da Sin don rage jerin sabani don cimma moriyar juna da samun nasara tare.Mao ta bayyana hakan ne a gun taron manema labarai na yau da kullum da aka gudanar yau Alhamis, yayin da take mayar da martani ga ra’ayin da aka gabatar, a taron kwamitin Tarayyar Turai game da “rage hadari” daga bangaren Sin.
Dangane da rahotannin dake cewa kawancen “Five Eyes Alliance” ko FVEY a takaice, ya zargi Sin da daukar wadanda ake kira “masu leken asiri”, Mao ta ce a matsayinsa na kawancen leken asiri mafi girma a duniya, FVEY ya dade yana gudanar da manyan ayyukan leken asiri a dukkanin fadin duniya.
Don haka abin mamaki ne kungiyar ta zargi kasar Sin da wai “barazanar leken asiri”.Bugu da kari, a cewar ma’aikatar harkokin wajen Sin, a yau Alhamis, ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya gana da ’yar takarar mukamin babban sakataren MDD, kuma tsohuwar shugabar Chile Verónica Michelle Bachelet Jeria a nan birnin Beijing. (Safiyah Ma)















Discussion about this post