Yanzu haka ana gudanar da taron masana ilmin harkokin kasar Sin na duniya karo na uku, a birnin Dunghuang na lardin Gansu, da ke arewa maso yammacin kasar Sin, inda wakilai sama da 300, da suka fito daga kasashe kusan 70, suke musaya a kan batutuwan da suka hada da musayar wayewar kai tsakanin Sin da sauran kasashen duniya.
Masanan sun kuma samu karin fahimta kan kasar Sin, ta ziyarce-ziyarce da ma sauran ayyukan da suka gudanar.Mahalarta taron sun bayyana cewa, hikimomin da ke cikin wayewar kan Sinawa, bisa jigon “Al’ummun duniya ‘yan uwan juna ne”, da “Hadin kai da zaman jituwa da juna”, sun samar da abin koyi ta fuskantar tunkarar kalubalolin duniya.
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
ADVERTISEMENT














Discussion about this post