Yayin da take shugabantar kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya a watan nan, kasar Sin za ta kira wani babban taron kwamitin a ranar 26 ga wata, mai taken “Kiyaye manufofi da ka’idojin kundin tsarin mulkin MDD, da karfafa tsarin kasa da kasa mai jigon MDD”, inda memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi, zai tafi New York don jagorantar taron.
Kuma yayin da yake New York, Wang Yi zai halarci taron rukunin abokai na tsarin shugabantar harkokin duniya mai suna “Group of Friends of Global Governance” wanda zai gudana a ranar 28 ga wata, tare da ganawa da sakatare janar na MDD gami da ministocin harkokin wajen wasu kasashe.
Kaza lika, zai ziyarci kasar Kanada daga ranar 28 zuwa 30 ga wata, bisa gayyatar takwararsa ta kasar, Anita Anand. (Murtala Zhang)















Discussion about this post