Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya amince da fitar da kusan naira biliyan 1 domin biyan haƙƙoƙin ma’aikatan bangaren shari’a da suka daɗe suna jiran a biya su.
An bayyana hakan ne yayin da shugabannin ƙungiyar ma’aikatan kotuna ta JUSUN reshen Kaduna ƙarƙashin jagorancin Auwalu Sarki suka kai masa ziyara a gidan gwamnati da ke Kaduna.
Kuɗaɗen da aka amince da biya sun haɗa da bashin albashin watannin Afrilu da Mayun shekarar 2021 da aka gada daga gwamnatin baya, kuɗaɗen hutun shekara na 2023 zuwa 2025, da kuma alawus-alawus na tufafi ga ma’aikatan shari’a.
Gwamna Uba Sani ya ce gwamnatinsa na ci gaba da ba da muhimmanci ga jin daɗin ma’aikata, inganta harkokin shari’a da kuma kyautata alaƙa tsakanin gwamnati da bangaren shari’a.















Discussion about this post