Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Sin, Lin Jian ya yi tsokaci game da gudanar da bikin sanya hannu kan yarjejeniyar kafa kungiyar hadin gwiwar fasahar AI ta duniya a birnin Shanghai jiya Alhamis, inda ya ce, Sin za ta yi aiki tare da sauran kasashen da suka kafa kungiyar don inganta kaddamar da aikinta da wuri.
Lin ya bayyana hakan ne a gun taron manema labarai na yau da kullun da aka gudanar yau Jumma’a.
Dangane da ikirarin shugaban Amurka Donald Trump na cewa “Sin ta tsoma baki a babban zaben Amurka”, Lin ya bayyana cewa, irin wannan ikirarin an dade ana tabbatar da cewa ba ya da tushe balle makama.
Game da sanarwar gwamnatin Trump cewa za ta rage lokacin zama na bizar ’yan jarida, kuma mai yiwuwa ’yan jaridar Sin suna cikin wadanda abin zai shafa kuwa, Lin ya ce Sin ta bukaci Amurka ta janye manufofinta na nuna wariya ga ’yan jaridar Sin nan take.
Bugu da kari, game da sanarwar Amurka ta yin gaban kanta wajen sake sanya karin haraji a kan kayayyakin Brazil, Lin ya bayyana cewa, babu wanda zai yi nasara a yakin haraji, kuma hakan ba ya dacewa da muradun kowane bangare.(Safiyah Ma)













