Wani babban jami’in kula da harkokin tattalin arziki na kasar Sin ya ce kasar za ta ci gaba da kara wa tattalin arzikin duniya tabbaci da daidaito da kuzari da ci gaba.
Mataimakin daraktan ofishin kula da harkokin kudi da tattalin arziki na kwamitin kolin JKS Han Wenxiu ne ya bayyana haka jiya, yayin taro kan ci gaban kasar Sin na 2026 da aka yi a Beijing.
A cewarsa, shirin raya tattalin arziki da zamantakewa na shekaru biyar-biyar na 15 na kasar Sin, na zaman taswirar kirkira da fadada samar da sabbin damarmaki tare da sauran sassan duniya.
Ya ce duk da rashin tabbas a duniya, kasar Sin za ta ci gaba da jajircewa wajen zurfafa gyare-gyare da fadada bude kofa cikin shekaru 5 masu zuwa. Ya kara da cewa, kasar za ta ci gaba da fadada ba da damar shiga kasuwarta da bude karin bangarori, musammam bangaren bayar da hidima, da kara fadada bude bangarori kamar na sadarwa da kiwon lafiya da ilimi.
Ya ce a matsayinta na wadda ta san ya kamata, kasar Sin ta yanke shawarar bude kasuwarta da fadada shigo da kayayyaki da soke haraji baki daya ga kasashe marasa karfi dake da huldar diplomasiyya da ita. (Mai fassara: FMM)















Discussion about this post