Kasar Sin ta bayar da tallafin sama da ton 3,000 na alkama da shinkafa, domin taimaka wa mutane masu rauni da fari da ambaliya da yaki suka shafa a Sudan ta Kudu.
Da yake jawabi yayin bikin mika kayayyakin, ministan kula da ayyukan jin kai da tunkarar ibtila’i na kasar Albino Akol Atak, ya ce gudunmuwar ta zo a muhimmin lokacin da kasar ke fuskantar matsalolin jin kai da suka yi mata katutu.
A nasa bangare, Willaiam Chan Achuil, mataimakin sakatare a ma’aikatar kula da ayyukan jin kai da tunkarar ibtila’i, ya ce tallafin abincin zai yi matukar karfafa wadatar abinci tsakanin wasu muhimman rukunoni, ciki har da mutanen da suka koma kasar da wadanda suka rasa matsugunansu da masu bukata ta musammam da iyalai masu rauni a fadin kasar.
Ya ce gudunmuwar na nuna hadin gwiwa mai karfi da ke tsakanin kasashen biyu, tare da bayyana kudurin Sin na tallafa wa kokarin kasar mafi kankantar shekaru a duniya a bangaren ayyukan jin kai da tabbatar da wadatar abinci.
Shi kuwa jakadan Sin a Sudan ta Kudu Ma Qiang cewa ya yi, ofishin jakadancin Sin da hadin gwiwar gwamnatin Sudan ta Kudu, sun raba kashi-kashi har 3 na kayayyakin agaji a rabin farko na bana.
Ya ce kashi na 4 na tallafin abincin wani muhimmin mataki ne wajen aiwatar da ayyukan hadin gwiwa 10 da aka sanar yayin taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika, kuma ya nuna kudurin kasar Sin na gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dan adama. (Fa’iza Mustapha)














