Sojojin Rundunar Hadin Gwiwa ta Arewa maso Yamma, Operation Fansan Yamma, sun ceto wani mutum da aka yi garkuwa da shi a Jihar Kaduna, tare da dakile wani harin ‘yan ta’adda a Jihar Sokoto, a wani ɓangare na ci gaba da ayyukan tabbatar da zaman lafiya a yankin Arewa maso Yamma.
Jami’in yaɗa labarai na Rundunar Hadin Gwiwar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar jiya a Gusau.
A cewarsa, sojojin Shiyya 1 sun samu kiran gaggawa a ranar 20 ga Agusta, 2026, bayan wasu ‘yan ta’adda sun yi garkuwa da wani mutum mai shekaru 43 a kusa da al’ummar Awon da ke Karamar Hukumar Kachia ta Jihar Kaduna.
Danja ya ce, “Nan take sojojin suka isa yankin tare da bin sawun ‘yan ta’addan zuwa cikin dazuzzukan da ke kewaye da yankin, lamarin da ya tilasta musu barin wanda suka yi garkuwa da shi tare da tserewa. Daga bisani, sojojin sun mika wanda aka ceto ga iyalansa.”
A wani lamarin na daban, sojojin Shiyya 2, tare da hadin gwiwar jami’an tsaron yankin, sun mayar da martani a ranar Juma’a ga wani harin ‘yan ta’adda da aka kai kauyen Kwaren Gamba da ke Karamar Hukumar Sabon Birni ta Jihar Sokoto.
Sojojin sun yi artabu da maharan tare da tilasta musu tserewa.
Ya kara da cewa, “A yayin bin sawun ‘yan ta’addan da suka tsere, an hallaka wani ɗan ta’adda guda ɗaya, yayin da sojoji suka ƙwato wayoyin hannu guda biyu, kuɗi, katin ATM, katin kiran waya da wasu kayayyaki a wurin da lamarin ya faru.”














