Dakarun rundunar sojin Nijeriya, sun kashe wasu manyan jagororin ‘yan bindiga biyu—Anaruwa da Gomina—tare da wasu mutum bakwai a jerin hare-haren da aka gudanar cikin kwanaki uku a jihohin Zamfara da Katsina.
Mataimakin Daraktan Yaɗa Labarai na rundunar, Sashe na 8 da Operation Fansan Yamma, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa.Ya bayyana cewa a Jihar Zamfara, dakaru daga sansanin gaba-gaba da ke Bagega sun kai wani farmaki mai haɗari a ƙaramar hukumar Anka, wanda ya kai ga kashe ‘yan ta’adda bakwai, ciki har da shahararrun jagorori Anaruwa da Gomina.
An kuma bayyana cewa Anaruwa ƙanin shahararren jagoran ‘yan bindiga ne, Kachalla Idi Aiki.
Laftanar Kanal Olaniyi ya ƙara da cewa a farkon farmakin, dakarun sun yi arangama da ‘yan ta’addan a kan hanyar Bagega zuwa Anka, inda aka yi musayar wuta mai tsanani tsakanin ɓangarorin biyu.















Discussion about this post