Wani sabon rikicin siyasa na neman ɓarkewa a cikin NDC a Jihar Kano, yayin da shugaban jam’iyyar na jihar, Usaini Isa Mai Riga, ya ƙi amincewa da zargin yunkurin miƙa tsarin jam’iyyar ga tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.
Da yake magana a wata hira ta musamman ranar Litinin, Mai Riga ya bayyana cewa tattaunawar da aka yi domin tarbar Kwankwaso acikin jam’iyyar ta rushe bayan taruka biyu da aka gaza cimma matsaya kan batun iko da jagoranci.
A cewarsa, ana zargin tsohon gwamnan yana neman cikakken iko da tsarin jam’iyyar a jihar, abin da ya ce ba za a amince da shi ba.
“Yana so mu miƙa masa dukkan tsarin jam’iyyar, duk da irin sadaukarwar da muka yi lokacin da jam’iyyar ba ta da ƙarfi,” in ji Mai Riga.
Shugaban jam’iyyar ya jaddada cewa shugabannin da ke kan madafun iko a yanzu za su yi tsayin daka wajen kare matsayinsu, yana mai cewa za su bi duk hanyoyin doka domin ci gaba da riƙe tsarin jam’iyyar.















Discussion about this post