Dakarun rundunar shiyya 2 ta ‘Operation FANSAN YAMMA’ sun kashe ’yan ta’adda 10, sun kubutar da mutane 31 da aka yi garkuwa da su, tare da tarwatsa sansanonin ’yan bindiga da kuma kwato makamai da alburusai a wasu hare-hare da suka kai a jihohin Zamfara da Katsina.
Rundunar sojin Nijeriya ta tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da mukaddashin mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta 8 Division da shiyya 2 Operation FANSAN YAMMA, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ya sanya wa hannu, sannan aka rabawa manema labarai a Gusau, jihar Zamfara, ranar Lahadi.
Sanarwar ta ce, an ceto mutanen ne bayan wani harin sama na musamman da bangaren sojojin sama na rundunar ya kai, sannan aka bi da farmakin kasa kan maɓoyar ’yan ta’addan da ke yankin yammacin dajin Bagega.
Mutanen da aka kuɓutar, waɗanda aka ce sun shafe makonni da dama a hannun masu garkuwa da mutanen, sun fito ne daga ƙananan hukumomin Maga, Gummi, Zuru, Wasugu, Bukuyyum da Anka na jihar Zamfara, da kuma wasu sassan jihohin Sokoto da Kebbi.
Rundunar sojin ta ce an bai wa waɗanda aka ceto kulawar lafiya kuma za a miƙa su ga iyalansu nan ba da jimawa ba.















Discussion about this post