Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi watsi da kudirin mafi karancin albashi na N100,000 da kungiyar gwamnonin Nijeriya (NGF) ta gabatar, tana mai cewa albashin da zai dace da rayuwa a halin tattalin arzikin yanzu ya kamata ya kai kusan naira miliyan daya.
Mai magana da yawun NLC, Benson Upah, ne ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da jaridar ‘The PUNCH’ a ranar Lahadi.Martanin nasa ya biyo bayan kalaman shugaban NGF kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, wanda ya bayyana cewa gwamnoni na duba yiwuwar sanya sabon mafi karancin albashi na N100,000.
AbdulRazaq, yayin ziyarar gaisuwar Sallah ga Shugaba Bola Tinubu a Legas, ya ce gwamnoni na tattaunawa da gwamnatin tarayya da kungiyoyin kwadago domin cimma tsarin albashi da zai daidaita walwalar ma’aikata da kuma dorewar tattalin arziki.
A wani sako da ya wallafa a Facebook ranar Asabar, gwamnan ya kara da cewa kudirin ya samo asali ne daga hauhawar farashi, tsadar rayuwa da kuma karin nauyin da ma’aikatan Nijeriya ke fuskanta.
Da yake mayar da martani kan kudirin, Upah ya ce duk da cewa yunkurin gwamnoni na sake duba albashi abin yabo ne, amma N100,000 bai kai matsayin abin da ma’aikata ke bukata domin jure halin tattalin arzikin yanzu ba.
A cewarsa, “Mun yaba da tunanin gwamnan jihar Kwara na gabatar da wannan shawara, amma tabbas N100,000 ya yi kasa sosai da ainihin adadin da ya dace.”















Discussion about this post