Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya ce bai taɓa yi wa Shugaba Bola Tinubu alkawarin cewa zai koma jam’iyyar APC ba.
Wike ya ce abin da ya yi alƙawarin shi ne zai goyi bayan Tinubu a yunƙurinsa na neman wa’adi na biyu a matsayin shugaban ƙasa.
Da yake magana a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise a daren ranar Talata, Wike ya ce tun farko ya bayyana cewa zai goyi bayan Shugaban Ƙasar.
Ya ce, “Ban taɓa faɗa wa Shugaban Ƙasa cewa zan koma APC ba.
“Idan ina son koma APC, ba mutane irin su Hope ne za su faɗa min na koma ba.”
Wike ya kuma soki mutanen da ke matsa masa lamba kan ya koma APC, inda ya ce ba shi da shirin komawa jam’iyya mai mulki.














