A baya-bayan nan, tawagar likitocin Sin da ke aikin taimako a Nijar rukuni na 25, ta bayar da horo na farko kan agajin gaggawa da ya kai ingancin na kasa da kasa a asibitin the General Hospital of Reference na Nijar.
Wannan shi ne karo na farko da aka gudanar da irin wannan horo a wurin.A yayin bikin bude kwas din, darektan asibitin Mamane Daou, ya gode wa tawagar likitocin Sin bisa goyon bayan da ta dade tana bayarwa, kuma ya bayyana cewa ma’aikatan lafiya na wurin na bukatar karfafa kwarewarsu ta gudanar da aikin jinya bisa ka’ida, kuma wannan horon ya samar wa asibitin wani dandalin horaswa na musamman da ya kai ingancin na kasa da kasa.
Shugabar tawagar likitocin Sin a Nijar, Huang Huiqiao ta bayyana cewa, tawagarta tana kokarin bayar da horo don ganin an aiwatar da ka’idojin agajin gaggawa na kasa da kasa a wurin, tare da mai da hankali kan horar da ma’aikatan lafiya masu kwarewar samar da agajin gaggawa a wurin. (Bilkisu Xin)














Discussion about this post