Yusuf Buhari, ɗan tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya samu tikitin jam’iyyar APC domin tsayawa takarar kujerar Majalisar Wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Daura/Sandamu/Mai’adua a zaɓen 2027.
Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa (NAN) ya ruwaito cewa Yusuf ya samu tikitin ba tare da hamayya ba, bayan wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Jihar Katsina a ranar Talata, 28 ga Afrilu, inda aka amince da shi baki ɗaya a matsayin ɗan takarar jam’iyyar.
Shugaban Kwamitin Yarjejeniya na Yankin Daura, Alhaji Ahmed Dangiwa, tsohon Ministan Gidaje da Raya Birane, ne ya sanar da wannan matsaya.
Da yake jawabi bayan amincewa da Yusuf, Mannir Musa, Shugaban APC na Ƙaramar Hukumar Mai’adua, ya buƙaci mambobin jam’iyyar su karɓi sakamakon cikin kwanciyar hankali.
“Na roƙi dukkan mutanenmu da su yi biyayya su karɓi matsayar da kwamitin da masu ruwa da tsaki suka cimma cikin fahimta mai kyau. Ya kamata mu haɗa kai domin haɗin kan jam’iyya da cigaban al’ummarmu,” in ji shi.
Ya kuma roƙi Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, da ya tallafa wa waɗanda ba su samu tikiti ba domin su ci gaba da yi wa al’ummarsu hidima.
Musa ya buƙaci waɗanda aka ba tikiti ta hanyar yarjejeniya da su yi aiki tukuru domin wakiltar al’ummarsu yadda ya kamata idan aka zaɓe su.
Ya ƙara da cewa sauran ‘yan takarar da suka samu tikiti kai tsaye sun haɗa da Nasir Yahaya domin kujerar Sanatan Daura, da Mustapha Musa domin kujerar Majalisar Dokokin Jihar Katsina mai wakiltar Mai’adua.
A nasa jawabin, Yusuf Buhari ya gode wa mambobin jam’iyyar bisa amincewar da suka nuna masa, tare da alƙawarin yin wakilci nagari idan aka zaɓe shi.















Discussion about this post