ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Yusuf Buhari Ya Samu Tikitin Takarar Majalisar Wakilan Nijeriya A Jam’iyyar APC

by Muhammad
2 months ago

Yusuf Buhari, ɗan tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya samu tikitin jam’iyyar APC domin tsayawa takarar kujerar Majalisar Wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Daura/Sandamu/Mai’adua a zaɓen 2027.

Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa (NAN) ya ruwaito cewa Yusuf ya samu tikitin ba tare da hamayya ba, bayan wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Jihar Katsina a ranar Talata, 28 ga Afrilu, inda aka amince da shi baki ɗaya a matsayin ɗan takarar jam’iyyar.

Shugaban Kwamitin Yarjejeniya na Yankin Daura, Alhaji Ahmed Dangiwa, tsohon Ministan Gidaje da Raya Birane, ne ya sanar da wannan matsaya.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi bayan amincewa da Yusuf, Mannir Musa, Shugaban APC na Ƙaramar Hukumar Mai’adua, ya buƙaci mambobin jam’iyyar su karɓi sakamakon cikin kwanciyar hankali.

“Na roƙi dukkan mutanenmu da su yi biyayya su karɓi matsayar da kwamitin da masu ruwa da tsaki suka cimma cikin fahimta mai kyau. Ya kamata mu haɗa kai domin haɗin kan jam’iyya da cigaban al’ummarmu,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

Ya kuma roƙi Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, da ya tallafa wa waɗanda ba su samu tikiti ba domin su ci gaba da yi wa al’ummarsu hidima.

Musa ya buƙaci waɗanda aka ba tikiti ta hanyar yarjejeniya da su yi aiki tukuru domin wakiltar al’ummarsu yadda ya kamata idan aka zaɓe su.

Ya ƙara da cewa sauran ‘yan takarar da suka samu tikiti kai tsaye sun haɗa da Nasir Yahaya domin kujerar Sanatan Daura, da Mustapha Musa domin kujerar Majalisar Dokokin Jihar Katsina mai wakiltar Mai’adua.

A nasa jawabin, Yusuf Buhari ya gode wa mambobin jam’iyyar bisa amincewar da suka nuna masa, tare da alƙawarin yin wakilci nagari idan aka zaɓe shi.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Next Post
Jami’in MDD Ya Yaba Da Manufar Soke Harajin Kwastam Ta Kasar Sin A Matsayin Kyakkyawan Ci Gaba

Jami’in MDD Ya Yaba Da Manufar Soke Harajin Kwastam Ta Kasar Sin A Matsayin Kyakkyawan Ci Gaba

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026
Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.