ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Yusuf Buhari Ya Samu Tikitin Takarar Majalisar Wakilan Nijeriya A Jam’iyyar APC

by Muhammad
3 months ago

Yusuf Buhari, ɗan tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya samu tikitin jam’iyyar APC domin tsayawa takarar kujerar Majalisar Wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Daura/Sandamu/Mai’adua a zaɓen 2027.

Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa (NAN) ya ruwaito cewa Yusuf ya samu tikitin ba tare da hamayya ba, bayan wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Jihar Katsina a ranar Talata, 28 ga Afrilu, inda aka amince da shi baki ɗaya a matsayin ɗan takarar jam’iyyar.

Shugaban Kwamitin Yarjejeniya na Yankin Daura, Alhaji Ahmed Dangiwa, tsohon Ministan Gidaje da Raya Birane, ne ya sanar da wannan matsaya.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi bayan amincewa da Yusuf, Mannir Musa, Shugaban APC na Ƙaramar Hukumar Mai’adua, ya buƙaci mambobin jam’iyyar su karɓi sakamakon cikin kwanciyar hankali.

“Na roƙi dukkan mutanenmu da su yi biyayya su karɓi matsayar da kwamitin da masu ruwa da tsaki suka cimma cikin fahimta mai kyau. Ya kamata mu haɗa kai domin haɗin kan jam’iyya da cigaban al’ummarmu,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Ya kuma roƙi Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, da ya tallafa wa waɗanda ba su samu tikiti ba domin su ci gaba da yi wa al’ummarsu hidima.

Musa ya buƙaci waɗanda aka ba tikiti ta hanyar yarjejeniya da su yi aiki tukuru domin wakiltar al’ummarsu yadda ya kamata idan aka zaɓe su.

Ya ƙara da cewa sauran ‘yan takarar da suka samu tikiti kai tsaye sun haɗa da Nasir Yahaya domin kujerar Sanatan Daura, da Mustapha Musa domin kujerar Majalisar Dokokin Jihar Katsina mai wakiltar Mai’adua.

A nasa jawabin, Yusuf Buhari ya gode wa mambobin jam’iyyar bisa amincewar da suka nuna masa, tare da alƙawarin yin wakilci nagari idan aka zaɓe shi.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Jami’in MDD Ya Yaba Da Manufar Soke Harajin Kwastam Ta Kasar Sin A Matsayin Kyakkyawan Ci Gaba

Jami’in MDD Ya Yaba Da Manufar Soke Harajin Kwastam Ta Kasar Sin A Matsayin Kyakkyawan Ci Gaba

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.