Kamfanin rarraba wutar lantarki na Nijeriya (TCN) ya mayar da wutar lantarki a Jihar Kebbi bayan samar da wata sabuwar hanyar rarraba wuta.
An dawo da wutar ne daga yankin Kaduna-Mando ta hanyar layin wutar 132kV Zaria-Funtua-Gusau.
Jihar Kebbi ta shafe sama da mako guda ba tare da wutar lantarki ba bayan iska mai ƙarfi da ruwan sama suka lalata layin wutar Kainji-Birnin Kebbi.
TCN ta fara dawo da wutar a ranar Talata, kodayake wutar na ɗaukewa zuwa lokaci-lokaci.
Mazauna jihar da ’yan kasuwa sun bayyana farin cikinsu kan dawowar wutar, inda suka bayyana cewa hakan zai rage musu wahalhalun da suka fuskanta a baya.
TCN ta ce za a ci gaba da amfani da wannan hanyar har sai injiniyoyi sun kammala gyaran layin wutar Kainji-Birnin Kebbi da ya lalace.













