Jam’iyyar APC a jihar Kaduna ta nuna damuwarta bisa rahotannin lalata motoci da ofisoshin jam’iyyar tare kuma da kaiwa magoya bayanta hari a jihar.
A wata sanarwar da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar, Sani Ɗan Azare ya sanyawa hannu, jam’iyyar ta yi kira ga rundunar ƴansanda ta ƙasa da ragowar jami’an tsaro da su yi bincike domin gano abin da ya faru tare da ɗaukar hukunci a kan duk wanda aka samu da hannu wajen kar hare-haren.
Jam’iyyar ta APC ta ce tana sane tare da bibiyar duk wani rahoto na kaiwa mambobinnta hari, kuma tana shawartar jami’an tsaro da su yi bincike domin tabbatar da gano waɗanda ake zargi.
“Jihar Kaduna ta yi nisa wajen daina yin siyasar kabilanci da ta addini wanda hakan yana kawo tsaiko wajen samar da zaman lafiya a faɗin jihar kuma wannan aikin da aka yi na samar da zaman lafiya a jihar ba za mu bari wasu su lalata ba ta hanyar lalata kayan mutane tare da tayar da hargitsi” in ji Sani Ɗan Azare.
Ya ce, jam’iyyar APC a jihar Kaduna ta duƙufa wajen ganin ta wanzar da zaman lafiya da bin doka da oda tare kuma da kira da ragowar jam’iyyun siyasa da ma ƴan siyasa a jihar da su zama masu bin doka.
Ya ce “Muna shawartar magoya bayanmu da ƙungiyoyin jam’iyya a faɗin jihar Kaduna da su kwantar da hankulansu tare da gujewa duk wani abu da zai tayar da hankali ko mayar da martani.
“Duk wanda yake da wata shaida ko yasan masu aikata ba daidai ba, ya yi gaggawar kai rahoto ga hukumomin da suka kamata. A ƙarshe ya ce babu wani abu da ya fi zaman lafiya muhimmanci a jihar Kaduna. A bayyana gaskiya, a yi bincike sannan a ɗauki matakin da ya kamata a kan duk wanda aka samu da laifi.”














