An sake bude Kwalejin Ilimi ta Jihar Kwara, don ci gaba da gudanarwa bisa umarnin gwamnatin jihar duba da samun ci gaba a fannin tsaro.
Umarnin buɗewar yana ƙunshe ne a cikin wata takardar sanarwa da aka fitar a ranar Litinin kuma jaridar PUNCH ta gani.
Takardar, mai lamba: CEO/ADMIN/27/Vol.1/268, mai kwanan wata 2 ga Fabrairu, 2026, Mataimakiyar Magatakarda, Misis Lawal Taibat Saka-Bolanta ce ta sanya mata hannu.
Takardar, wacce aka aika wa ma’aikata da ɗalibai kuma aka fitar daga ofishin Magatakarda, ta bayyana cewa, kwalejin ta koma aiki nan take.
ADVERTISEMENT















Discussion about this post