• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

by Aisha Seyoji
2 years ago
in Ra'ayoyi
0
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

A halin yanzu ‘Yan Nijeriya na ta dakon ganin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada ministocitoci. Shin a ganinka/ki, wane ne mafi cancanta a nada shi Minista daga Jiharku. Fadi suna da kuma takaitaccen bayani kan zabin naka ko naki.

LUKMAN B. ADAM: Pantami Ya Fi Cancanta Daga Gombe

A jiharmu ta Gombe kam gaskiya babu wanda ya cancanta daya wuce Prof Isa Ali Ibrahim Pantami. Domin kuwa shi ne kadai ya san damuwan talakawa kuma yake taimaka musu sannan kuma Mutum ne wanda ba ya kyamar mutane ga kuma ilimi ta kowane bangaren rayuwa da Allah ya ba shi kuma sannan ga shi ya yi mun gani duk Nijeriya tunda ake ba a taba yin Minista da ya yi aikin da ya yi ba.

Kai a takaice dai Nijeriyar ma kanta irin Prof Isa Ali muke bukata ba ‘yan bulkara da karya da rainin hankali ba.

CMRD MOHD GADDAFI AWWAL: El-Rufai Ya Kamata A Nada Daga Kaduna

Gaskiya ni dai a nawa ra’ayin, Malam Nasiru El-Rufai ya fi cancanta a nada daga Kaduna, jajirtacce ne kowa ya san shi, ba ya wasa a kan aikinsa.

SADEEK RUFAI DANGUGUWA: Ina So A Dauki Kwankwaso Daga Kano

Ina son Engr Dr Rabiu Musa Kwankwaso na Jahar Kano ya kasance daya daga cikin Ministocin da za a nada. Ba don komai ba, sai don kyakkyawan yakinin da nake dashi a kansa, saboda Kwankwaso mutum ne mai sanin makamar aiki ta kowacce siga, ba zan riya cewa Kwankwaso ya kai makura ba, domin kaiwa makura siffa ce da Ubangiji Ya kabance kanshi da ita, amma tabbas Kwankwaso na da dukkan ‘Capacity’ din zama daya daga cikin Ministocin kasar nan.

JAFAR S. HASSAN KARABA: Gwamma A Nada Sani Sha’aban A Kaduna

Mu a Kaduna wanda nake ganin ya fi kowa cancanta a nada shi shi ne Sani Sha’aban, shi muke so, saboda ya fi Nasiru sanin hakkin al’umma wallahi.

IT’Z JAMEEL MOHD: Ba Ruwanmu Da Wani Minista, Fatanmu Farashin Kayan Masarufi Ya Sauka

Kullum fata muke farashin kayan masa rufi ya yi kasa talaka ya ji dadi a Nijeriya. Babu ruwanmu da wani minister. Buhun masara 48k, Shinkafa 35k, Litar Mai 600, Ina talakan Nijeriya zai sa kansa?

APC Change Change: Ganduje Da Gawuna Muke So A Nada Daga Kano

A gaskiya mu dai a ganinmu babu wanda ya cancanta a nada a matsayin minister daga Jihar Kano illa Ganduje da Gawuna.

ABDUL’AZIZ MOHAMMED: Allah Ya Zaba Mana Mafi Alheri Daga Gombe

Da farko dai ina miki barka da wannan lokaci, Allah ya datar da mu amin. Ni dai a nawa bangaren a gaskiya addu’a nake, duk wanda zai zama alkhairi ga al’ummar Jihar Gombe da ma kasa gaba daya Allah ya tabbatar mana da shi amin.

ALIYU SULAIMAN: A Nada Mana Isah Yuguda Daga Jihar Bauchi

Ni dai nawa zabin a Jihar Bauchi shi ne: Isah Yuguda. Sabida a Bauchi babu wanda bai san Jarumtarsa ba. A lokachin Isah Yuguda a Bauchi, ‘Principal’ din ‘Secondary school’ ma na hawa mota. Amma ban da zamanin Bala. Ya yi minista a baya na ‘abiation’, an ga rawar da ya taka. Yanzu ma idan ya samu dama, zai sake yin abin da ya saba. Sabida shi dan mai kishin mutanensa ne a zuciya.

UMAR ABDULLAHI: Allah Ya Sa A Nada Mana Hazikai

Ina miki fatan alkhairi, Allah ya sa mu dai a sa mana hazikai masu aikin da aka nada su wanda za mu ga canji na alkhairi a kasarmu Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MinistociTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ancelotti Zai Zama Kociyan Tawagar Brazil A 2024

Next Post

Manoman Tumatur 70,000 Na Bukatar Tallafin Gwamnatin Kano – Yadakwari

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

3 months ago
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

7 months ago
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

8 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

8 months ago
BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

8 months ago
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Ra'ayoyi

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

9 months ago
Next Post
Manoman Tumatur 70,000 Na Bukatar Tallafin Gwamnatin Kano – Yadakwari

Manoman Tumatur 70,000 Na Bukatar Tallafin Gwamnatin Kano - Yadakwari

LABARAI MASU NASABA

Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.