ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Yi Bitar Nasarorin Da Aka Cimma Yayin Taron Kolin SCO Na Tianjin

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Wang Yi

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi bitar nasarorin da aka cimma yayin taron kolin kungiyar hadin kai ta Shanghai ko SCO na shekarar nan ta 2025 da ya gudana a birnin Tianjin.

Taron na SCO irin sa mafi girma da aka gudanar tun kafuwar kungiyar a shekarar 2001, ya hallara shugabannin kasashe sama da 20, da jagororin hukumomin kasa da kasa 10.

Wang, wanda kuma memba ne a hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS, ya ce an amince da kudurorin bunkasa ayyukan SCO tsakanin shekarun 2026 zuwa 2035, wanda za su saita alkiblar bunkasa kungiyar cikin shekaru 10 masu zuwa.

ADVERTISEMENT

Yayin taron manema labarai da ya jagoranta tare da babban sakataren kungiyar ta SCO mista Nurlan Yermekbayev, Wang Yi ya ce an fitar da sanarwar taron na bana, mai kunshe da goyon baya ga nasarar da aka cimma, ta kawo karshen yakin duniya na biyu. Kazalika, cikin wata sanarwar ta daban da aka fitar, kungiyar SCO ta bayyana cikakken goyon bayanta ga tsarin cudanyar cinikayya tsakanin mabanbantan sassa.

Har ila yau, a cewar Wang, yayin taron, an kaddamar da sabbin cibiyoyin SCO guda hudu, wadanda aka dorawa alhakin shawo kan barazanar tsaro da sauran kalubale, da aikin dakile laifukan da ake yi tsakanin iyakokin kasashe daban daban, da kyautata tsaron bayanai, da karfafa hadin gwiwa a fannin dakile yaduwar miyagun kwayoyi.

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

Bugu da kari, kasashe membobin kungiyar sun amince da kafa bankin bunkasa harkokin SCO, wanda a cewar Wang, zai yi matukar bunkasa samar da ababen more rayuwa, da raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummun kasashe membobin kungiyar.

Dadin dadawa, kasar Sin ta sha alwashin kafa sabon dandalin hadin gwiwa, da cibiyoyi masu nasaba da makamashi, da samar da ci gaba marar gurbata yanayi, da tattalin arzikin dijital, da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha, da ilimi mai zurfi, da na koyar da sana’o’i da fasahohi. An kuma fitar da tsarin ingiza ci gaba mai inganci, wanda ya kunshi sassa irinsu na makamashi, da masana’antun sarrafa hajoji ba tare da gurbata yanayi ba, da tattalin arzikin dijital, da kirkirarriyar basira ko AI da kirkire-kirkiren fasaha. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Wang Yi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Goyon Bayan Ci Gaban Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Bude Kasuwarta Ga Gyadar Sha Zawa Daga Nahiyar Afrika
Wang Yi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar
  • Sulaiman
    Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu

MASU ALAKA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

June 16, 2026
Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

June 16, 2026
Sin Na Goyon Bayan Ci Gaban Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Ci Gaban Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa

June 16, 2026
Next Post
Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

June 16, 2026
Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

June 16, 2026
Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

June 16, 2026
Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu

Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu

June 16, 2026
Sin Na Goyon Bayan Ci Gaban Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa

Sin Na Goyon Bayan Ci Gaban Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa

June 16, 2026
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kira Zaman Gaggawa A Ranar 23 Ga Yuni Kan Matsalar Tsaro

June 16, 2026
Sin Ta Bude Kasuwarta Ga Gyadar Sha Zawa Daga Nahiyar Afrika

Sin Ta Bude Kasuwarta Ga Gyadar Sha Zawa Daga Nahiyar Afrika

June 16, 2026
Sojoji Sun Fatattaki Lakurawa, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa A Kebbi

Sojoji Sun Fatattaki Lakurawa, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa A Kebbi

June 16, 2026
Gwamna Radda Ya Ziyarci Matar Janar Rabe Da Aka Ceto, Ya Yaba Wa Sojoji

Gwamna Radda Ya Ziyarci Matar Janar Rabe Da Aka Ceto, Ya Yaba Wa Sojoji

June 16, 2026
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

Peter Obi Ya Nemi A Janye Hukuncin Kotu Kan Soke Rijistar ADC

June 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.