ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi: Akwai Bukatar Mayar Da Shekara Ta 2026 Ta Zama Muhimmiyar Shekara Ga Dangantakar Sin Da Amurka

by Sulaiman
1 month ago
Xi

Da safiyar yau Alhamis 14 ga watan nan na Mayu, a babban zauren jama’a na birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban Amurka Donald Trump wanda ke ziyarar aiki a kasar Sin.

Xi ya nuna cewa, a halin yanzu ana ci gaba da fuskantar sauye-sauye da ba a taba gani irinsa ba a karnin da ya gabata, kuma yanayin kasa da kasa yana cikin rudani da sauye-sauye. Shin ko Sin da Amurka za su iya wuce “tarkon Thucydides”, wato ra’ayin bunkasar wata kasa mai tasawo ta yi takara da maye gurbin wata kasa mai wadata? Kuma ko za su iya kirkiro sabon salo na dangantakar manyan kasashe? Shin ko za su iya hada kai don fuskantar kalubalen duniya, da kuma samar da karin kwanciyar hankali ga duniya tare? Shin ko za su iya yin la’akari da jin dadin al’ummomin kasashen biyu, da makomar bil’adama cikin hadin gwiwa don bude kyakkyawar makoma ga dangantakar kasashen biyu?

Wadannan tambayoyi ne na tarihi, da duniya da kuma jama’a suke shakka, kuma suna cikin tambayoyin da shugabannin manyan kasashe ke bukatar su ba da amsa tare.

ADVERTISEMENT

Xi ya jaddada cewa, muradun bai daya tsakanin Sin da Amurka sun fi muhimmanci fiye da sabanin ra’ayi, kuma nasarar kowannensu dama ce ga juna, kana kwanciyar hankali a dangantakar Sin da Amurka yana amfanawar duniya. Ya kamata bangarorin biyu su zama abokan hadin gwiwa maimakon abokan hamayya, su kuma taimaki juna da samun ci gaba tare, da kuma bin hanyar da ta dace tsakanin manyan kasashe a sabon zamani. Xi yana mai fatan yin hadin gwiwa da shugaba Trump, don aiwatar da musayar ra’ayi kan manyan batutuwan da suka shafi kasashen biyu da kuma duniya, tare da jagorantar bunkasar dangantakar Sin da Amurka yadda ya kamata, don mayar da shekara ta 2026 ta zama shekara mai muhimmanci a tarihi ga samun kyakkyawar bunkasar dangantakar Sin da Amurka.

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce yana fatan gudanar da babbar tattaunawa tare da shugaba Xi Jinping. A cewarsa, “Akwai wadanda ke ganin wannan ne taro mafi girma da aka taba gudanarwa. Duk da cewa mun fuskanci wahalhalu, amma za mu kamo bakin zaren. Za mu kai ga cimma kyakkyawar makoma tare.”

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

A kalaman nasa, Trump ya nanata kiran shugaba Xi da babban jagora. Yana mai cewa “Ina alfahari da kasancewa abokinka, kuma alaka tsakanin Sin da Amurka za ta ci gaba da inganta sama da lokutan baya.”

Bugu da kari, a yau Alhamis 14 ga wata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Donald Trump suka ziyarci wurin ibada na Tiantan tare.

Xi, ya yi maraba da Trump a babban ginin Qiniandian, sun kuma dauki hoto tare a filin da ke gaban babban ginin wurin ibadar, daga nan kuma suka kewaya cikin babban ginin tare.

Xi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
Next Post
Sin Na Fatan Raya Huldar Sin Da Amurka a Sabon Matsayi Tare Da Amurka

Sin Na Fatan Raya Huldar Sin Da Amurka a Sabon Matsayi Tare Da Amurka

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.