ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi: Akwai Bukatar Mayar Da Shekara Ta 2026 Ta Zama Muhimmiyar Shekara Ga Dangantakar Sin Da Amurka

by Sulaiman
1 month ago
Xi

Da safiyar yau Alhamis 14 ga watan nan na Mayu, a babban zauren jama’a na birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban Amurka Donald Trump wanda ke ziyarar aiki a kasar Sin.

Xi ya nuna cewa, a halin yanzu ana ci gaba da fuskantar sauye-sauye da ba a taba gani irinsa ba a karnin da ya gabata, kuma yanayin kasa da kasa yana cikin rudani da sauye-sauye. Shin ko Sin da Amurka za su iya wuce “tarkon Thucydides”, wato ra’ayin bunkasar wata kasa mai tasawo ta yi takara da maye gurbin wata kasa mai wadata? Kuma ko za su iya kirkiro sabon salo na dangantakar manyan kasashe? Shin ko za su iya hada kai don fuskantar kalubalen duniya, da kuma samar da karin kwanciyar hankali ga duniya tare? Shin ko za su iya yin la’akari da jin dadin al’ummomin kasashen biyu, da makomar bil’adama cikin hadin gwiwa don bude kyakkyawar makoma ga dangantakar kasashen biyu?

Wadannan tambayoyi ne na tarihi, da duniya da kuma jama’a suke shakka, kuma suna cikin tambayoyin da shugabannin manyan kasashe ke bukatar su ba da amsa tare.

ADVERTISEMENT

Xi ya jaddada cewa, muradun bai daya tsakanin Sin da Amurka sun fi muhimmanci fiye da sabanin ra’ayi, kuma nasarar kowannensu dama ce ga juna, kana kwanciyar hankali a dangantakar Sin da Amurka yana amfanawar duniya. Ya kamata bangarorin biyu su zama abokan hadin gwiwa maimakon abokan hamayya, su kuma taimaki juna da samun ci gaba tare, da kuma bin hanyar da ta dace tsakanin manyan kasashe a sabon zamani. Xi yana mai fatan yin hadin gwiwa da shugaba Trump, don aiwatar da musayar ra’ayi kan manyan batutuwan da suka shafi kasashen biyu da kuma duniya, tare da jagorantar bunkasar dangantakar Sin da Amurka yadda ya kamata, don mayar da shekara ta 2026 ta zama shekara mai muhimmanci a tarihi ga samun kyakkyawar bunkasar dangantakar Sin da Amurka.

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce yana fatan gudanar da babbar tattaunawa tare da shugaba Xi Jinping. A cewarsa, “Akwai wadanda ke ganin wannan ne taro mafi girma da aka taba gudanarwa. Duk da cewa mun fuskanci wahalhalu, amma za mu kamo bakin zaren. Za mu kai ga cimma kyakkyawar makoma tare.”

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A kalaman nasa, Trump ya nanata kiran shugaba Xi da babban jagora. Yana mai cewa “Ina alfahari da kasancewa abokinka, kuma alaka tsakanin Sin da Amurka za ta ci gaba da inganta sama da lokutan baya.”

Bugu da kari, a yau Alhamis 14 ga wata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Donald Trump suka ziyarci wurin ibada na Tiantan tare.

Xi, ya yi maraba da Trump a babban ginin Qiniandian, sun kuma dauki hoto tare a filin da ke gaban babban ginin wurin ibadar, daga nan kuma suka kewaya cikin babban ginin tare.

Xi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Sin Na Fatan Raya Huldar Sin Da Amurka a Sabon Matsayi Tare Da Amurka

Sin Na Fatan Raya Huldar Sin Da Amurka a Sabon Matsayi Tare Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.