ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi: Akwai Bukatar Mayar Da Shekara Ta 2026 Ta Zama Muhimmiyar Shekara Ga Dangantakar Sin Da Amurka

by Sulaiman
2 months ago
Xi

Da safiyar yau Alhamis 14 ga watan nan na Mayu, a babban zauren jama’a na birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban Amurka Donald Trump wanda ke ziyarar aiki a kasar Sin.

Xi ya nuna cewa, a halin yanzu ana ci gaba da fuskantar sauye-sauye da ba a taba gani irinsa ba a karnin da ya gabata, kuma yanayin kasa da kasa yana cikin rudani da sauye-sauye. Shin ko Sin da Amurka za su iya wuce “tarkon Thucydides”, wato ra’ayin bunkasar wata kasa mai tasawo ta yi takara da maye gurbin wata kasa mai wadata? Kuma ko za su iya kirkiro sabon salo na dangantakar manyan kasashe? Shin ko za su iya hada kai don fuskantar kalubalen duniya, da kuma samar da karin kwanciyar hankali ga duniya tare? Shin ko za su iya yin la’akari da jin dadin al’ummomin kasashen biyu, da makomar bil’adama cikin hadin gwiwa don bude kyakkyawar makoma ga dangantakar kasashen biyu?

Wadannan tambayoyi ne na tarihi, da duniya da kuma jama’a suke shakka, kuma suna cikin tambayoyin da shugabannin manyan kasashe ke bukatar su ba da amsa tare.

ADVERTISEMENT

Xi ya jaddada cewa, muradun bai daya tsakanin Sin da Amurka sun fi muhimmanci fiye da sabanin ra’ayi, kuma nasarar kowannensu dama ce ga juna, kana kwanciyar hankali a dangantakar Sin da Amurka yana amfanawar duniya. Ya kamata bangarorin biyu su zama abokan hadin gwiwa maimakon abokan hamayya, su kuma taimaki juna da samun ci gaba tare, da kuma bin hanyar da ta dace tsakanin manyan kasashe a sabon zamani. Xi yana mai fatan yin hadin gwiwa da shugaba Trump, don aiwatar da musayar ra’ayi kan manyan batutuwan da suka shafi kasashen biyu da kuma duniya, tare da jagorantar bunkasar dangantakar Sin da Amurka yadda ya kamata, don mayar da shekara ta 2026 ta zama shekara mai muhimmanci a tarihi ga samun kyakkyawar bunkasar dangantakar Sin da Amurka.

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce yana fatan gudanar da babbar tattaunawa tare da shugaba Xi Jinping. A cewarsa, “Akwai wadanda ke ganin wannan ne taro mafi girma da aka taba gudanarwa. Duk da cewa mun fuskanci wahalhalu, amma za mu kamo bakin zaren. Za mu kai ga cimma kyakkyawar makoma tare.”

LABARAI MASU NASABA

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

A kalaman nasa, Trump ya nanata kiran shugaba Xi da babban jagora. Yana mai cewa “Ina alfahari da kasancewa abokinka, kuma alaka tsakanin Sin da Amurka za ta ci gaba da inganta sama da lokutan baya.”

Bugu da kari, a yau Alhamis 14 ga wata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Donald Trump suka ziyarci wurin ibada na Tiantan tare.

Xi, ya yi maraba da Trump a babban ginin Qiniandian, sun kuma dauki hoto tare a filin da ke gaban babban ginin wurin ibadar, daga nan kuma suka kewaya cikin babban ginin tare.

Xi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnan Nasarawa Ya Sallami Kwamishinoni Shida Na Majalisar Zartarwar Jihar
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio
  • Sulaiman
    Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

MASU ALAKA

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba
Daga Birnin Sin

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

July 22, 2026
An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

July 22, 2026
Asibitin Tafi Da Gidanka Na Jirgin Ruwan Sin Ya Nufi Kasashen Afrika Da Kudancin Asiya Domin Bayar Da Hidimomin Jin Kai
Daga Birnin Sin

Asibitin Tafi Da Gidanka Na Jirgin Ruwan Sin Ya Nufi Kasashen Afrika Da Kudancin Asiya Domin Bayar Da Hidimomin Jin Kai

July 22, 2026
Next Post
Sin Na Fatan Raya Huldar Sin Da Amurka a Sabon Matsayi Tare Da Amurka

Sin Na Fatan Raya Huldar Sin Da Amurka a Sabon Matsayi Tare Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar

Gwamnan Nasarawa Ya Sallami Kwamishinoni Shida Na Majalisar Zartarwar Jihar

July 23, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Akpabio

Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

July 23, 2026
Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

July 22, 2026
Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

July 22, 2026
An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

July 22, 2026
Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

July 22, 2026
Asibitin Tafi Da Gidanka Na Jirgin Ruwan Sin Ya Nufi Kasashen Afrika Da Kudancin Asiya Domin Bayar Da Hidimomin Jin Kai

Asibitin Tafi Da Gidanka Na Jirgin Ruwan Sin Ya Nufi Kasashen Afrika Da Kudancin Asiya Domin Bayar Da Hidimomin Jin Kai

July 22, 2026
Iran Ta Musanta Zargin Ɓoye Makaman Nukiliya A Dutsen Kolang

Iran Ta Musanta Zargin Ɓoye Makaman Nukiliya A Dutsen Kolang

July 22, 2026
An Kafa Cibiyar Binciken Wayewar Kai Ta Duniya

An Kafa Cibiyar Binciken Wayewar Kai Ta Duniya

July 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.