Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya karfafa wa Sinawa matasa gwiwar tsara burikansu ta yadda za su dace da ayyukan raya kasar.Xi Jinping wanda kuma shi ne sakatare janar na kwamitin kolin JKS kuma shugaban hukumar koli ta sojin kasar, ya bayyana haka ne cikin amsar wasikar da ya aikewa wakilan wadanda suka samu Lambar Karramawa ta Matasa, gabanin Ranar Matasa ta Kasar Sin a gobe Litinin.
Haka zalika cikin wasikar, shugaba Xi ya aike da sakon gaisuwa ga matasan da ke fadin kasar.Kwamitin koli na kungiyar matasa ta JKS ya bayyana a yau cewa, kungiyar na da kimanin mambobi miliyan 78.34 zuwa karshen shekarar 2025, inda a bara ta samu sabbin mambobi kusan miliyan 9.14.
Bisa bayanan da kwamitin koli kungiyar ya fitar, zuwa karshen bara, kungiyar na da kimanin hukumomin miliyan 5.15 a fadin kasar. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post