Kyaftin ɗin tawagar ƙwallon ƙafa ta Argentina, Lionel Messi, ya yi watsi da jita-jitar da ake yaɗawa cewa Hukumar Kwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA) na goyon bayan ƙasarsa domin ta lashe gasar Kofin Duniya.
Ya ce nasarorin da Argentina ta samu sun samo asali ne daga jajircewa da aiki tuƙuru.Messi ya bayyana hakan ne bayan Argentina ta samu nasarar doke Ingila a wasan kusa da na ƙarshe da suka buga ranar Laraba.
Ya ce nasarar da tawagar ta samu ta samo asali ne sakamakon haɗin kai da ƙoƙarin ‘yan wasanta.
Tun bayan wasan zagayen ‘yan 16, inda Argentina ta doke Egypt, aka fara yaɗa jita-jitar cewa alƙalan wasa na yi wa ƙasar alfarma. Sai dai Messi ya musanta wannan zargi.
A cewarsa, nasarorin Argentina sun samo asali ne daga aiki tuƙuru, jajircewa da haɗin kan ‘yan wasa a dukkanin wasannin da suka buga.
Argentina za ta yi ƙoƙarin kare kambunta yayin da za ta kara da Spain a wasan ƙarshe da za a buga ranar Lahadi, yayin da Ingila za ta kara da Faransa a wasan neman matsayi na uku a ranar Asabar.














