Kwamitin Sulhu na MDD ya bayyana matukar damuwa game da tsananta da karuwar sarkakiya da ma yadda yanayin hare-haren ta’addanci ke sauyawa.
Cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin ya fitar jiya, Kwamitin Sulhun ya sake nanata cewa, ta’addanci daya ne daga cikin barazana mafiya tsanani ga zaman lafiya da tsaro a duniya, yana mai bayyana damuwa game da yadda ake amfani da sabbin fasahohi kamar na intanet da sadarwar tauraron dan Adam da kadarori na intanet da jirage mara matuki, a ayyukan ta’addanci.
An fitar da sanarwar ce bayan taron da kwamitin ya yi kan ta’addanci, wanda ya yi daidai da cika shekaru 25 da hare-haren ranar 11 ga watan Satumba da aka kai Amurka.
Da yake jawabi ga taron, mukaddashin mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Sun Lei, ya ce ya kamata kasa da kasa su karfafa hadin kai da hadin gwiwa, da nacewa wajen dakile alamomi da abubuwan da ke haddasa ta’addanci.
Ya ce yayin da ake tsaurara daukar matakan tsaro, ya kamata a mayar da hankali wajen kawar da yanayi da muhallin rainon ayyuakn ta’addanci.Game da barazanar fasaha da ke bullowa kuwa, ya ce kasar Sin na kira da a inganta ka’idojin shugabanci da tsare-tsaren tafiyar da harkoki da taimaka wa kasashe masu tasowa karfafa karfinsu na amfani da sabbin fasahohi wajen yaki da ta’addanci. (Fa’iza Mustapha)













