Yayin da zaɓukan kakar shekarar 2027 ke ƙara dumrowa, masu ruwa da tsaki a jihar Kaduna, sun gargaɗi musamman matasa da ƴan siyasa a jihar kan yin amfani da matasan domin yin jagaliyanci a lokacin yaƙin neman zaɓe da kuma bayan zaɓukan.
Ɗaya daga cikin masu ruwan da tsaki, ƙungiyar Jama’atu Nasril Islam da ke jihar, ta bakin Murshid a ƙungiyar kuma mai riƙon ƙwarya, a hirasa da LEADERSHIP Hausa ya ce ” Wannan zaɓe ne 2027, wajibi ne, mu gayawa mutane gaskiya, musamman kan yadda wasu ƴan siyasar, ke bai wa matasa ƙwayoyi da su kamar Gariyo, domin yi masu jagalanciyanci a lokacin zaɓukan,” A cewarsa, addinin Musulnci ya haramta aikata dabbacin siyasa duba da cewa, aikata hakan, na janyo rashin zaman lafiya kashe waɗanda ba su ji ba su kuma gani ba, domin kawai ƴan siyasa, cimma burukansu na siyasa.Murshid ya kafa hujja da Aya ta 5:32 a cikin suratul Al-Ma’idah da ta ce, kashe rai ɗaya, tamkar kashe alumma ce, baki ɗaya.
Ya ce, kamata yayi duk matashin da ya kira matasan su yi masa jagalanci, su ce masu, su bai wa ƴaƴansu su yi masu, inda ya ƙara da cewa, JNI za ta kuma bi ƴan siyasar su sheda masu cewar, duk wanda ƙungiyar ta samu ya bai wa matasan ƙwaya, Jama’atu wallahi, ba za ta barshi ba, idan har ta gane, ƴan siyasar, suna bai wa matasan Barandami da ƙwaya domin yi masu dabar siyasa.A ɓangaren addinin Kirista kuwa, fitaccen Fasto a Kaduna Dakta Yohanna Buru ya shedawa LEADERSHIP Hausa ya ce,”Babban saƙonsa akan wannan batun, ina gargaɗin ƴan siyasa kam yan da su daina amfani da ƴaƴan talakawa a matsayin ƴan dabar siyasa ko ƴan banga,” In ji shi.
A cewarsa, litaffin Bible mai tsarki, ya yi tir da akita dabar siyasa, wacce ke haddasa tayar da hargitsi a tsakanin alumma da kuma kashe rayukan jama’a, musamman duba da faɗin Aya ta, Matthew 11:12.Buru ya kuma yanko Ayoyin Isaiah 3:14 da Ezekiel 22:7, da suka yi tir da ɗabi’ar duk wani mai neman madafun iko da yayi amfani da ƙarfi k tuwo, kan tusawa marasa ƙarfi, domin samun shugabanci.
Ya jaddada cewa, idan har dabar siyasa abu ne mai kyau, kamata ya yi ƴan siyasar, su fito da nasu ƴaƴan su ba su makamai su yi dabar.Ya yi kira ga matasa da su farka daga baccin jahilci da fatara, su gane cewa, makomar rayuwarsu ta fi gaban dan kudin da ƴan siyasa ke basu na lokaci kalilan.Ita kuwa cibiyar sansanci a tsakanin addinai da ke a jihar Kaduna, ɗaya daga cikin Daraktocinta Mista Samson Auta a zantawarsa da LEADERSHIP Hausa gargaɗin kira ta yi ga matasan da su kaucewa yaɗa kalaman ƙiyaya a lokacin zaɓukan da bayansa, domin kaucewa haddasa yamutsi a cikin alumma.
Shi kuwa Darskta Janar na ƙungiyar da ke samar da kyakyawar alaƙa da haɗa kan alumimin A rewacin Nijeriya da kuma wanzar da zaman lafiya wato ACI Dakta Idris Abdullahi, a hirar da LEADERSHIP Hausa ya ce, ƙungiyar tun a farkon wannan shekarar ta fara wayar da kan matasa da ke a shiyyar Arewa maso Yamma, musamman ta hanyar gudanar da gangamin wayar da kansu, na ilolin kaucewa gujewa ƴan sisyar da za su ba su, kuɗi ƴan ƙalina domin yin dabar siyasa.
Kazalika, a ɓangaren masatsa ɗaya daga cikin ƴan majalisar Hakin Tudun Wada Kaduna wato garkuwan matasan yankin Alh. Nura Haruna ya ce, “Mu a gundumar yankin tuni, muka yi nisa wajen faɗakar da matasan da ke a yankin, wanda ya ce, yana da yaƙinin, ba za a tsinci matasan, a cikin wannan hali ba“ in shi.
Ya yi nuni da cewa, yawanci rashin aikin yi ne, ke sanya irin waɗanan ƴan siyasar ke yin amfani da wasu matasan domin jagaliyar siyasa.Shi ma wani shugaban matasan yankin Kawo a Kaduna Alh Murtala Umar Kawo ya ce, suma a yankin tuni, sun duƙufa wajen yin gangamin wayar da kan matasan yankin kan su gujewa bari a yi amfani da su, yin bangar siyasa.Ya ce, duk mutumin da ke tara ƴan daba, ana cin mutuncin mutane, musamman a lokacin zaɓe da ke hadda ɗaukar rayukan mutane ba ma tare da shi, a siyasa.
“Ina son matasan su gane cewa, irin waɗannan ƴan siyasar sun keɓe ƴaƴansu sun kuma kai su, makarantu masu tsada suna kula da rayuwarsu, amma su matasan ƴaƴan talakawa, suna nan suna yawo, abincin da ma za su ci, ya gagare su”. A cewarsa.
Ya ce, idan da matasa za su gane su rungumi sana’a da yafi masu, amma kar su bari, wasu ƴan siyasar su rinƙa basu ƙwaya da Tabar Wiwi da sauran kayan maye, kuma lokacin da za a fita yaƙin neman zaɓen su ɗauki makamai su shiga gaba domin yin dabar siyasa, bayan alhali su ƴan siyasar na cikin motocinsu suna shan isakar ACkuma a cikin motocin nasu suna cin dambun nama da madara, su kuma matasan, an bar cikinsu cike da hayaƙin kayan maye.
Shi ma Kwamandan NDLEA reshen Jihar Kaduna Muhammad Maijama, ya yi wannan gargaɗin, a hirarsa da LEADERSHIP Hausa inda ya ce,” Zamu sanya ƙafar Wando ɗaya, da duk wani mutum, ko matasan da ke shan kayan maye, a lokacin zaɓukan da kuma bayansu, domin yiwa ƴan siyasa a jahar dabar siyasa,” Inji shi.
A yanzu,“Mun ƙara ƙaimi na yin aiki ba dare ba rana, domin mu ci gaba da wayar da kan ɗaukacin alummar jihar, musamman matasan da ke yin tu’ammali da kayan maye cewar, duk wanda hukumar ta samu da hannu ya tayar da hankali a lokacin zaɓukan da kuma bayan zaɓukan, zai ɗanɗana kuɗarsa,” A cewar kwamandan.
Mai jama’a, ya ja hankalin musamman iyayen irin waɗannan matasan da ke yin tu’ammali da kayan maye, cewa, su, ja kunnen ƴaƴansu, domin duk wanda hukumar ta kama ya haddasa rikici a lokacin zaɓukan, zai fuskanci hukunci, kamar yadda dokar ƙasa, ta tanadar.













