A yau Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya shirya liyafar ban girma a zauren jama’a da ke Beijing, domin maraba da shugaban Amurka, Donald Trump, a ziyarar aiki da ya kawo kasar Sin.
Da yake jawabi a wajen liyafar, shugaban Xi Jinping ya ce dangantakar Sin da Amurka ita ce mafi muhimmancin alakar diflomasiyya a duniya a yanzu haka.
Yana mai cewa, “Dole ne mu tabbatar da alakar tana gudana yadda ya kamata, kuma kada mu wargaza ta,” inda ya kara da cewa, Sin da Amurka duka za su iya cin moriya daga hadin gwiwa, kana za su tafka asara idan aka rungumi fito-na-fito.
Har ila yau, ya ce, “Ya kamata kasashenmu biyu su kasance abokan hulda maimakon na hamayya.”
Shugaba Xi ya kuma bayyana cewa bangarorin biyu sun amince su gina alaka mai ma’ana tsakanin Sin da Amurka bisa manyan tsare-tsare na zaman lumana domin karfafa samun ingantaccen ci gaba mai dorewa ba tare da tangarda ba a dangantakar kasashen biyu, tare da kawo karin zaman lafiya, wadata da kuma bunkasa ga duniya. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post