A yau Litinin, babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping, ya yi rangadi a sabon yankin Xiong’an na raya sana’o’i dake lardin Hebei na arewacin kasar Sin.
Xi Jinping, ya gane wa idanunsa yadda aikin ginin yankin sabbin sana’o’i ke gudana, kana ya ziyarci kamfanin China Huaneng Group, da reshen makarantar babbar sakandare ta Beijing mai lamba 4 dake Xiong’an, don fahimtar yanayin ci gaban sabon yankin na Xiong’an.
Kazalika, ya gaisa da wakilan jami’ai, da ma’aikatan hukumomin da aka sauyawa matsaguni wadanda wasu suka riga suka fara aiki a Xiong’an, wasu kuma ana kan gina wuraren gudanar da ayyuka, a wani bangare na ayyukan ragewa birnin Beijing nauyin gudanar da wasu ayyuka masu karancin amfani, ta yadda birnin zai ci gaba da rike matsayinsa na fadar mulkin kasa. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post