ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Buba Marwa Ya Yaki ‘Yan Siyasa Masu Raba Wa Matasa Kwaya – Matasan Arewa A Kudu

by Sulaiman
4 years ago
Arewa

Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa da ke yankin Kudancin Nijeriya a Jihar Legas, ta yi kira ga shugaban Hukumar Yaki da Sha da Safarar Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), Buba Marwa ya mike haikan wajen yaki da bata-garin ‘yan siyasa da ke raba kwayoyi ga matasa don ingiza su bangar siyasa.

A cewar gamayyar, bata-garin ‘yan siyasar suna amfani da kwaya wajen jirkita tunanin matasa don su cimma muradunsu na son zuciya.

  • Tattaunawa: Hulda Da Kasar Sin Muhimmin Ginshiki Ne Ga Ajandar Samar Da Abinci A Afrika

Shugaban Gamayyar Matasan, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanchi, wanda ya yi kiran a zantawarsa da manema labarai, ya kara da cewa, “Tun da yanzu an shiga lokacin siyasa gadan-gadan, bata-garin ‘yan siyasa suna nan babu abin da suke yi illa sayen miyagun kwayoyi suna raba wa matasa.

ADVERTISEMENT

Don haka muke kira ga ga Shugaban NDLEA, Buba Marwa ya kara mikewa tsaye wajen sa ido a kan yadda wadannan bata-garin ‘yan siyasar suke amfani da kwaya su lalata tunanin matasa, su ingiza su cikin bangar siyasa don cimma burinsu.”

Wakazalika, gamayyar ta yi kira ga wakilan al’umma a majalisun dokoki a matakai daban-daban su kafa wata doka da za ta hana bangar siyasa, “Kuma muna kira ga sanatoci da ‘yan majalisar dokoki su ji tsoron Allah su yi dokar da za ta hana bangar siyasa domin ceton matasa.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Don babu ‘yan siyar da suke daukar ‘ya’yansu su je da su wajen taron siyasa domin gudun abin da zai je ya dawo. Wannan shi ne rokon da muke yi a gare su, domin amana ce suka dauka kuma Allah ba zai bar su ba sannan muna sake kira ga shugabanni musamman wadanda suka fito daka arewacin kasarmu su ji tsoron haduwarsu da Allah, domin sun san yadda yankinsu yake ciki, amma sun gaza yin abin da ya dace.”

Gamayyar ta kara da cewa, hatta su kansu ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyya mai mulki ta APC sun san ba a yi abubuwan da suka kamata wajen magance matsalar tsaron da ake fama da ita a kasar nan ba.

“Mun dade muna gaya wa wakilanmu da sauran shugabanninmu na arewa cewa ba a yin abubuwan da suka kamata wajen magance matsalar nan ta kashe-kashen jama’a. Ga shi yanzu hatta su kansu wasu daga cikin ‘yan takarar shugaban kasa na APC sun yi tsokaci a kan kashe-kashe da sace-sacen mutane da ake yi wanda gwamnati ba ta yi abin da ya dace ta yi ba na kawo karshen wadannan masifun. Mun tabbatar da cewa mutum daya ba zai iya ba dole sai an hada karfi da karfe.

“Dan haka muke kara kai kukanmu ga Ubangiji da ya ba mu shugabanni nagari wadanda za su hana yi mana kisan gillah kuma muna kira da gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da ta yi dokar hana deligate a siyasar Nijeriya kafin ta sauka domin wannanma zai taimaka wa alumma.

“Haka nan muna kara kiga ga matasa su kula saboda sun ga yadda tsarin siyasarmu yake, ba a kulawa da su sai in za a saka su bangar siyasa a ba su kwaya.” In ji shi.

Marwa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Mayakan Ukraine Na Gudu Daga Fagen Fafafata Wa Da Rasha

Mayakan Ukraine Na Gudu Daga Fagen Fafafata Wa Da Rasha

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.