ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Buba Marwa Ya Yaki ‘Yan Siyasa Masu Raba Wa Matasa Kwaya – Matasan Arewa A Kudu

by Sulaiman
4 years ago
Arewa

Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa da ke yankin Kudancin Nijeriya a Jihar Legas, ta yi kira ga shugaban Hukumar Yaki da Sha da Safarar Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), Buba Marwa ya mike haikan wajen yaki da bata-garin ‘yan siyasa da ke raba kwayoyi ga matasa don ingiza su bangar siyasa.

A cewar gamayyar, bata-garin ‘yan siyasar suna amfani da kwaya wajen jirkita tunanin matasa don su cimma muradunsu na son zuciya.

  • Tattaunawa: Hulda Da Kasar Sin Muhimmin Ginshiki Ne Ga Ajandar Samar Da Abinci A Afrika

Shugaban Gamayyar Matasan, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanchi, wanda ya yi kiran a zantawarsa da manema labarai, ya kara da cewa, “Tun da yanzu an shiga lokacin siyasa gadan-gadan, bata-garin ‘yan siyasa suna nan babu abin da suke yi illa sayen miyagun kwayoyi suna raba wa matasa.

ADVERTISEMENT

Don haka muke kira ga ga Shugaban NDLEA, Buba Marwa ya kara mikewa tsaye wajen sa ido a kan yadda wadannan bata-garin ‘yan siyasar suke amfani da kwaya su lalata tunanin matasa, su ingiza su cikin bangar siyasa don cimma burinsu.”

Wakazalika, gamayyar ta yi kira ga wakilan al’umma a majalisun dokoki a matakai daban-daban su kafa wata doka da za ta hana bangar siyasa, “Kuma muna kira ga sanatoci da ‘yan majalisar dokoki su ji tsoron Allah su yi dokar da za ta hana bangar siyasa domin ceton matasa.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Don babu ‘yan siyar da suke daukar ‘ya’yansu su je da su wajen taron siyasa domin gudun abin da zai je ya dawo. Wannan shi ne rokon da muke yi a gare su, domin amana ce suka dauka kuma Allah ba zai bar su ba sannan muna sake kira ga shugabanni musamman wadanda suka fito daka arewacin kasarmu su ji tsoron haduwarsu da Allah, domin sun san yadda yankinsu yake ciki, amma sun gaza yin abin da ya dace.”

Gamayyar ta kara da cewa, hatta su kansu ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyya mai mulki ta APC sun san ba a yi abubuwan da suka kamata wajen magance matsalar tsaron da ake fama da ita a kasar nan ba.

“Mun dade muna gaya wa wakilanmu da sauran shugabanninmu na arewa cewa ba a yin abubuwan da suka kamata wajen magance matsalar nan ta kashe-kashen jama’a. Ga shi yanzu hatta su kansu wasu daga cikin ‘yan takarar shugaban kasa na APC sun yi tsokaci a kan kashe-kashe da sace-sacen mutane da ake yi wanda gwamnati ba ta yi abin da ya dace ta yi ba na kawo karshen wadannan masifun. Mun tabbatar da cewa mutum daya ba zai iya ba dole sai an hada karfi da karfe.

“Dan haka muke kara kai kukanmu ga Ubangiji da ya ba mu shugabanni nagari wadanda za su hana yi mana kisan gillah kuma muna kira da gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da ta yi dokar hana deligate a siyasar Nijeriya kafin ta sauka domin wannanma zai taimaka wa alumma.

“Haka nan muna kara kiga ga matasa su kula saboda sun ga yadda tsarin siyasarmu yake, ba a kulawa da su sai in za a saka su bangar siyasa a ba su kwaya.” In ji shi.

Marwa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Mayakan Ukraine Na Gudu Daga Fagen Fafafata Wa Da Rasha

Mayakan Ukraine Na Gudu Daga Fagen Fafafata Wa Da Rasha

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.