ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakan Kwastam Na Musamman A Dukkanin Fadin Yankin Cinikayya Cikin ’Yanci Na Hainan Ya Jawo Hankalin Duniya Sosai

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Sin

Yau Alhamis 18 ga watan Disamba ne, aka fara aiwatar da matakan kwastam na musamman a dukkanin fadin yankin cinikayya cikin ’yanci na Hainan, wanda hakan ya zamo sabon muhimmin mataki a manufar kasar Sin ta fadada bude kofarta ga duniya a sabon zamanin da muke ciki.

Ganin yadda ake kara aiwatar da manufofin gata na kwastam, da saukaka matakan kasuwanci gami da zirga-zirgar ababen hawa, da kuma kyautata ayyukan sa ido yadda ya kamata, aiwatar da matakan kwastam na musamman a dukkanin fadin yankin cinikayya cikin ’yanci na Hainan, zai iya haifar da dimbin alfanu ga kamfanoni, da daidaikun mutane, har ma da habakar tattalin arzikin duniya baki daya, al’amarin da ya janyo mabiya da masoya da dama a duniya.

Tun tuni kamfanoni masu jarin waje, sun fara gudanar da ayyukansu a lardin Hainan, ganin yadda za su samu sabbin damarmaki, saboda fara aiwatar da matakan kwastam na musamman a dukkanin fadin yankin cinikayya cikin ’yanci na Hainan. Alkaluma sun nuna cewa, daga watan Janairu zuwa Satumban bana, adadin jarin waje da aka yi amfani da shi a lardin Hainan, ya karu da kaso 42.2 bisa dari, kan na makamancin lokaci na bara.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ayyana ranar 18 ga watan Disambar bana don fara aiwatar da matakan na da babbar ma’ana. Saboda a makamanciyar ranar a shekarar 1978, cikakken zama na uku na kwamitin kolin JKS na 11, ya kafa tarihin kaddamar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofar kasar Sin ga duniya.

A halin yanzu, wato bayan shekaru 47, ra’ayin nuna bangaranci, da na ba da kariyar cinikayya na kara kamari, har ma dunkulewar tattalin arzikin duniya baki daya na fuskantar koma-baya. A irin wannan halin da ake ciki, fara aiwatar da matakan kwastam na musamman a dukkanin fadin yankin cinikayya cikin ’yanci na Hainan ya kafa tarihi, wanda ya zama wani muhimmin mataki da kasar Sin ta dauka, wajen inganta bude kofa ga duniya, da kafa budadden salon raya tattalin arzikin duniya. (Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Sulaiman
    Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya
  • Sulaiman
    Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

MASU ALAKA

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
Daga Birnin Sin

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya
Daga Birnin Sin

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 

Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 

LABARAI MASU NASABA

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.