Wasu da ake zargin ‘yan ta’addan Lukarawa ne sun tare hanyar Mokwa zuwa New Bussa a Jihar Neja a ranar Litinin, lamarin da ya haifar da fargaba a tsakanin direbobi, fasinjoji da mazauna yankin.
Rahotanni sun ce maharan, waɗanda ake kyautata zaton suna da yawa sun zo a kan babura, inda suka tare hanyar yankin Zurgurma da ke Ƙaramar Hukumar Mashegu, inda suka dakatar da motocin da ke wucewa tare da tilasta matafiya bin wasu hanyoyi.
An kuma ce maharan sun shiga ƙauyen Zurgurma da wasu maƙwabtan ƙauyuka, inda suka jefa tsoro a tsakanin jama’a tare da tsayar da zirga-zirga da sauran al’amuran yau da kullum.
Lamarin ya haifar da tashin hankali yayin da jama’a suka tsere domin tsira darayukansu, sannan harkokin kasuwanci da zirga-zirga suka tsaya na ɗan lokaci.
Kakakin ‘yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da cewa jami’an tsaro sun kai ɗauki cikin gaggawa.
Ya ce zuwan jami’an tsaro ya sa maharan suka tsere, inda suka gudu zuwa daji a yankin.
A halin yanzu, hukumomin tsaro na ci gaba da sa ido a yankin domin daƙile sake aukuwar irin wannan hari da kuma tabbatar da tsaron jama’a da masu amfani da hanyar.















Discussion about this post