Sojojin rundunar haɗin gwiwa ta Operation FANSAN YAMMA sun kashe wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne guda biyu tare da kama wasu a Jihar Kaduna.
Sun gudanar da aikin ne tsakanin ranar 20 zuwa 21 ga watan Yuni a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin yaƙi da ‘yan bindiga da masu satar shanu da sauran laifuka a Arewa maso Yamma.
Rahoton sojoji ya ce sun samu bayanan sirri kan satar shanu, inda suka yi artabu da ‘yan bindiga.
Sun kashe biyu daga cikinsu, sannan suka ƙwato dabbobin da aka sace tare da mayar wa masu su.
An kuma ƙwace makamai da harsasai yayin aikin.
Sai dai wani farar hula ya rasa ransa a lokacin artabun yayin da maharan ke ƙoƙarin tserewa.
A wani aiki na daban da sojojin suka yi, sun kama wasu biyu da ake zargi da taimaka wa ‘yan bindiga.
A ranar 21 ga watan Yuni kuma, sojoji sun bi sahun wasu ɗauke da makamai, inda suka kama wasu biyu da ke taimakawa ‘yan bindiga.
An kuma ƙwato babura da na’urorin sadarwa.
Sojoji sun ce lamarin ya haifar da tashin hankali a yankin, inda wasu fusatattun matasa suka yi ƙoƙarin kai wa kadarorin gwamnati hari, amma jami’an tsaro sun daƙile su tare da wanzar da zaman lafiya.
Hukumomi sun yaba wa dakarun bisa nasarorin da suka samu, suna mai cewa za a ci gaba da kai hare-hare kan miyagun mutane domin inganta tsaro a yankin.














Discussion about this post