ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2 Tare Da Kama Wasu A Kaduna

by Sadiq
56 minutes ago

Sojojin rundunar haɗin gwiwa ta Operation FANSAN YAMMA sun kashe wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne guda biyu tare da kama wasu a Jihar Kaduna.

Sun gudanar da aikin ne tsakanin ranar 20 zuwa 21 ga watan Yuni a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin yaƙi da ‘yan bindiga da masu satar shanu da sauran laifuka a Arewa maso Yamma.

Rahoton sojoji ya ce sun samu bayanan sirri kan satar shanu, inda suka yi artabu da ‘yan bindiga.

ADVERTISEMENT

Sun kashe biyu daga cikinsu, sannan suka ƙwato dabbobin da aka sace tare da mayar wa masu su.

An kuma ƙwace makamai da harsasai yayin aikin.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Lakurawa Suka tare Babbar Hanyar Zuwa Neja, Tare Da Jefa Jama’a Cikin Firgici

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Watsi Da Kiran Obi Na Buƙatar Tinubu Ya Yi Murabus

Sai dai wani farar hula ya rasa ransa a lokacin artabun yayin da maharan ke ƙoƙarin tserewa.

A wani aiki na daban da sojojin suka yi, sun kama wasu biyu da ake zargi da taimaka wa ‘yan bindiga.

A ranar 21 ga watan Yuni kuma, sojoji sun bi sahun wasu ɗauke da makamai, inda suka kama wasu biyu da ke taimakawa ‘yan bindiga.

An kuma ƙwato babura da na’urorin sadarwa.

Sojoji sun ce lamarin ya haifar da tashin hankali a yankin, inda wasu fusatattun matasa suka yi ƙoƙarin kai wa kadarorin gwamnati hari, amma jami’an tsaro sun daƙile su tare da wanzar da zaman lafiya.

Hukumomi sun yaba wa dakarun bisa nasarorin da suka samu, suna mai cewa za a ci gaba da kai hare-hare kan miyagun mutane domin inganta tsaro a yankin.

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja
Manyan Labarai

Yadda Lakurawa Suka tare Babbar Hanyar Zuwa Neja, Tare Da Jefa Jama’a Cikin Firgici

June 23, 2026
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Watsi Da Kiran Obi Na Buƙatar Tinubu Ya Yi Murabus
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Watsi Da Kiran Obi Na Buƙatar Tinubu Ya Yi Murabus

June 23, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 47 Da ISWAP Suka Sace A Jihar Borno
Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 47 Da ISWAP Suka Sace A Jihar Borno

June 23, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2 Tare Da Kama Wasu A Kaduna

June 23, 2026
‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Yadda Lakurawa Suka tare Babbar Hanyar Zuwa Neja, Tare Da Jefa Jama’a Cikin Firgici

June 23, 2026
Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Watsi Da Kiran Obi Na Buƙatar Tinubu Ya Yi Murabus

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Watsi Da Kiran Obi Na Buƙatar Tinubu Ya Yi Murabus

June 23, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 47 Da ISWAP Suka Sace A Jihar Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 47 Da ISWAP Suka Sace A Jihar Borno

June 23, 2026
’Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 28 A Jihar Filato

An Kashe Mutane 19 A Wani Sabon Hari A Filato

June 23, 2026
Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 3 Da Makamai A Kogi

Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 3 Da Makamai A Kogi

June 23, 2026
Tinubu Ya Yi Murabus Saboda Ya Gaza A Kan Matsalar Tsaro – Peter Obi

Tinubu Ya Yi Murabus Saboda Ya Gaza A Kan Matsalar Tsaro – Peter Obi

June 23, 2026
An Bude Bikin Baje Kolin Hada-Hadar Samar Da Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Karo Na Hudu

An Bude Bikin Baje Kolin Hada-Hadar Samar Da Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Karo Na Hudu

June 22, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jaddada Aniyarta Na Ƙin Sulhu Da ‘Yan Ta’adda

Gwamnatin Zamfara Ta Jaddada Aniyarta Na Ƙin Sulhu Da ‘Yan Ta’adda

June 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.